عن عبد الله بن عمر رضي الله عنهما قال: «صَلَّيتُ معَ رسول الله -صلَّى الله عليه وسلم- رَكعَتَين قَبل الظُّهر، وَرَكعَتَين بَعدَها، ورَكعَتَين بعد الجُمُعَةِ، ورَكعَتَينِ بَعدَ المَغرِب، وَرَكعَتَينِ بَعدَ العِشَاء». وفي لفظ: «فأمَّا المغربُ والعشاءُ والجُمُعَةُ: ففي بَيتِه». وفي لفظ: أنَّ ابنَ عُمَر قال: حدَّثَتنِي حَفصَة: أنَّ النبِيَّ -صلَّى الله عليه وسلم-: «كان يُصَلِّي سَجدَتَين خَفِيفَتَينِ بَعدَمَا يَطلُعُ الفَجر، وكانت سَاعَة لاَ أَدخُلُ على النبيَّ -صلَّى الله عليه وسلم- فِيهَا».
[صحيح] - [متفق عليه بجميع رواياته]
المزيــد ...

Daga Abdullahi Dan Umar Allah ya yarda dasu: yace: "Na yi salla tare da Manzo tsira da aminci su tabbata a gare shi; raka'a biyu kafi azahar da wasu raka'a biya bayan azahar, da raka'a biyu bayan jumaa, da raka'a biyu bayan Magariba, da raka'a biyu bayan issha" A wani lafazin: "Magariba da Issha'i da Jumua a gidansa yake yi" A wani lafazin: Dan Umar yace: Hafsa ta bani labarin cewa Annabi tsira da amincin Allah: " ya kasance yana yin raka'oi biyu masu sauki bayan fitowat alfijir. lokaci ne da ya kasance bana shiga wajen Annabi tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi".
Ingantacce ne - Buhari da Muslim ne suka rawaito shi da dukkan ruwayoyin sa

Bayani

Wannan hadisai biyu suna bayani ne akan sunnoni da ake jeranta su tare da salloli biyar,hakan kuwa shi ne Azahar tana da raka'a hudu,biyu kafin ayi ta,biyu kuma bayan an yi ta,Jumu'a ma tana da raka'a biyu bayan an kammala ta,Magariba ma tana da raka'a biyu a bayanta,Issha'i ma tana da raka'a biyu a bayanta,amma sai dai sallolin da ake jerawa na Magariba da Issha'i,dana Asuba, da Juma'a,Manzo tsira da amincin Allah ya kasance yana yin su a gidansa ne. Abdullahi Dan Umar -Allah ya yarda da shi- yana da alaka da gidan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-saboda matsayin 'yar'uwarsa Hafsa a wajen Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-, ya kasance yakan shiga wajensa lokacin ibadarsa,sai dai yana kula ba koda yaushe yake shiga ba,saboda bin umarnin Allah Madaukaki:"Ya ku wadanda suka yi imani lallai abin da damarku ta mallaka,da wadanda basu isa mafarki daga cikinku ba suke neman izininku a lokuta guda uku,gabanin sallar Asuba" aya,sai ya zama ba mai shigar masa gabanin Alfijir,don ya ga yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ke yin salla,amma -saboda kwadayinsa da ilimi- ya kasance yana tambayar 'Yar'uwarsa"Hafsa"game da haka,sai ta bashi labarin cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- yana sallatar raka'a biyu masu sauki bayan fitowar Alfijir,sune sunnar sallar Asuba.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Swahili Yaran Tamili Yaran Tailand bushtu Asami السويدية الأمهرية
Manufofin Fassarorin