عن أبي هريرة رضي الله عنه قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم : (لولاَ أن أَشُقَّ عَلَى أُمَّتِي؛ لَأَمَرتُهُم بِالسِّوَاك عِندَ كُلِّ صَلاَة).
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...
Daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- yace: "(Ba don kar in matsawa al'umma ta ba da na umarce su da yin asuwaki yayin kowace salla)i
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]
Yana daga cikar kaunar Annabi ga al'ummarsa, da kwadayinsa wafjen yaga sun aikata duk wani abu wanda amfanin zai amfanar da su, shi ne ya kwadaitar da su akan yin asuwaki, saboda sanin fa'idojin asuwaki da Annabi ya yi, da amfanin yinsa a nan duniya da kuma lahira, har yayi kamar zai tilastawa al'ummarsa yin asuwaki a wagen alwala ko salla, saboda akwai ruwaya mai cewa ( tare da ko wace alwala), amma saboda tausayin Manzo sai ya ji tsoron Allah ya mai da shi wajibi, in basu yi ba su sami zunubi, sai bai tilasrta shi akan al'umma ba, amma duk da haka ya kwadaitar da su akan yin sa.