Karkasawa: Sirah da Tarihi .
+ -

عَنْ أَبِي بَكْرٍ الصِّدِّيقَ رَضيَ اللهُ عنه قَالَ:
نَظَرْتُ إِلَى أَقْدَامِ الْمُشْرِكِينَ عَلَى رُءُوسِنَا وَنَحْنُ فِي الْغَارِ، فَقُلْتُ: يَا رَسُولَ اللهِ لَوْ أَنَّ أَحَدَهُمْ نَظَرَ إِلَى قَدَمَيْهِ أَبْصَرَنَا تَحْتَ قَدَمَيْهِ، فَقَالَ: «يَا أَبَا بَكْرٍ، مَا ظَنُّكَ بِاثْنَيْنِ اللهُ ثَالِثُهُمَا».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 2381]
المزيــد ...

Daga Abubakar al-Siddiƙ - Allah Ya yarda da shi - ya ce:
Na kalli digadigan mushrikai akan kawunanmu alhali mu muna cikin kogo, sai na ce: Ya Manzon Allah da a ce ɗayansu zai kalii digadigansa zai ganmu a ƙarƙashin digadigansa, sai ya ce: «‌Ya Abubakar, me kake zato da mutum biyun da Allah Shi ne na ukunsu».

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2381]

Bayani

Sarkin muminai Abubakar al-Siddiƙ - Allah Ya yarda da shi - a lokacin hijira: Na kalli digadigan mushrikai alhali su suna tsaye akan kawunanmu a saman kogon Hira alhali mu muna cikinsa, sai na ce: Ya Manzon Allah da a ce ɗayansu zai yi duba zuwa ga digadigansa zai ganmu ƙarƙashin digadigansa, sai ya ce : Ya Abubakar, me kake zato da mutum biyu Allah ne na ukunsu da nasara da kuma taimako, da kiyayewa da kuma daidaita?!

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Darajar Abubakar al-Siddiƙ - Allah Ya yarda da shi - a abokantakarsa da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a hijirarsa da ya yi daga Makkah zuwa Madina, da kuma rabuwa da ya yi da iyalansa da kuma dukiyarsa.
  2. Tausayin Abubakar al-Siddiƙ - Allah Ya yarda da shi -, da kuma fagen soyayyarsa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, da kuma yadda ya jiye masa tsoro daga maƙiya.
  3. Wajabcin amincewa Allah - Mai girma da ɗaukaka -, da nutsuwa ga kiyayewarSa, da kuma kulawarSa bayan yin ƙoƙari a riƙar kiyayewa.
  4. Kulawar Allah - Maɗaukakin sarki - ga AnnabawanSa da masoyanSa, da kuma kiyayewarSa garesu da nasara, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: (Lallai ne Mu zamu taimaki Manzanninmu da waɗanda suka yi imani a rayuwar duniya da kuma ranar da masu shaida zasu tsaya).
  5. Faɗakarwa akan cewa duk wanda ya dogara ga Allah to Ya isar masa, zai taimake shi, kuma zai kiyaye shi.
  6. Cikar tawakkalin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ga Ubangijinsa, kuma cewa shi ne wanda ake dogaro gareShi, kuma ake fawwala al'amari gareShi.
  7. Gwarzantakar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, da kuma yadda yake sa zukata da rayuka nutsuwa.
  8. Guduwa da Addini dan jin tsoron maƙiyi, da kuma yin riƙo da sabubba.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Swahili Yaran Tailand Asami الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin