عن مُعاذة قالتْ: سألتُ عائشةَ رضي الله عنها فقلتُ: «مَا بَال الحَائِضِ تَقضِي الصَّوم، ولا تَقضِي الصَّلاة؟ فقالت: أَحَرُورِيةٌ أنت؟، فقلت: لَستُ بِحَرُورِيَّةٍ، ولَكنِّي أسأل، فقالت: كان يُصِيبُنَا ذلك، فَنُؤمَر بِقَضَاء الصَّوم، ولا نُؤْمَر بِقَضَاء الصَّلاَة».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Muazata -Allah ya yarda da ita-Ta ce: Na tambayi A'isha -Allah ya yarda da ita- sai nace:"Me ya sa mai yin haila ke rama azumi banda salla? sai ta ce: ke baharuriya ce? sai na ce Ni ba baharuriya bace, kawai dai tambaya nake.sai tace muma muna yin hailar,sai a umarce mu da rama azumi banda salla
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Muazata -Allah ya yarda da ita- ta tambayi A'isha -Alllah ya yarda da ita- game da dalilin da ya sa shari'a ta umarci mai haila ta rama azumin da ta sha amma baza ta rama sallolin da ta bari a lokacin da take haila ba,tare da cewa dukkanin ibadojin farilla ne, salla ma tafi azumi girman wajabci, kin banbantawa tsakanin salla da azumi a wajen ramuwa, shi ne mazahabin kawarij wanda ya ginu akan tsanantawa. Sai A'isha ta ce da ita: ke Baharuriya ce kina kudurce irin abin da suke kudurcewa. kuma kina tsanantawa kamar yadda suke tsanantawa? Sai tace:Ni Ba bahruriya bace, amma dai ina neman sani ne,sai A'isha tace: Mun kasance muna yin haila lokacin Manzo tsira da aminci Allah, kuma mun kasance ba ma yin azumi da salla a lokacinsa, sai ya umarce mu da rama azumi banda salla, da rama salla wajibi ne da Manzo bazai yi shiru ba. kamar tana cewa ne: bin umarnin sharia da kuma tsayuwa a inda sharia taIyakance shi yafi

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin