+ -

عن مُعاذة قالتْ: سألتُ عائشةَ رضي الله عنها فقلتُ: «مَا بَال الحَائِضِ تَقضِي الصَّوم، ولا تَقضِي الصَّلاة؟ فقالت: أَحَرُورِيةٌ أنت؟، فقلت: لَستُ بِحَرُورِيَّةٍ، ولَكنِّي أسأل، فقالت: كان يُصِيبُنَا ذلك، فَنُؤمَر بِقَضَاء الصَّوم، ولا نُؤْمَر بِقَضَاء الصَّلاَة».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Muazata -Allah ya yarda da ita-Ta ce: Na tambayi A'isha -Allah ya yarda da ita- sai nace:"Me ya sa mai yin haila ke rama azumi banda salla? sai ta ce: ke baharuriya ce? sai na ce Ni ba baharuriya bace, kawai dai tambaya nake.sai tace muma muna yin hailar,sai a umarce mu da rama azumi banda salla
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]

Bayani

Muazata -Allah ya yarda da ita- ta tambayi A'isha -Alllah ya yarda da ita- game da dalilin da ya sa shari'a ta umarci mai haila ta rama azumin da ta sha amma baza ta rama sallolin da ta bari a lokacin da take haila ba,tare da cewa dukkanin ibadojin farilla ne, salla ma tafi azumi girman wajabci, kin banbantawa tsakanin salla da azumi a wajen ramuwa, shi ne mazahabin kawarij wanda ya ginu akan tsanantawa. Sai A'isha ta ce da ita: ke Baharuriya ce kina kudurce irin abin da suke kudurcewa. kuma kina tsanantawa kamar yadda suke tsanantawa? Sai tace:Ni Ba bahruriya bace, amma dai ina neman sani ne,sai A'isha tace: Mun kasance muna yin haila lokacin Manzo tsira da aminci Allah, kuma mun kasance ba ma yin azumi da salla a lokacinsa, sai ya umarce mu da rama azumi banda salla, da rama salla wajibi ne da Manzo bazai yi shiru ba. kamar tana cewa ne: bin umarnin sharia da kuma tsayuwa a inda sharia taIyakance shi yafi

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin