عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«مِنْ حُسْنِ إِسْلَامِ المَرْءِ تَرْكُهُ مَا لَا يَعْنِيهِ».
[قال النووي: حديث حسن] - [رواه الترمذي وغيره] - [الأربعون النووية: 12]
المزيــد ...
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce:
«Yana daga kyan Musuluncin mutum yabar abin da babu ruwansa».
[قال النووي: حديث حسن] - [رواه الترمذي وغيره] - [الأربعون النووية - 12]
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa daga cikar kyawun Musuluncin musulmi da kuma cikar imaninsa, ya nisanci abin da bai shafe shi ba, kuma bai keɓance shi ba, bai da alaƙa da shi da kuma abin da ba zai amfane shi ba na maganganu da ayyuka, ko kuma abin da baruwansa da shi na al'amuran Addini da duniya, shagaltuwa da abin da bai shafi mutum ba wataƙila zai shagaltar da shi daga abin da akwai ruwansa a ciki, ko ya kai shi zuwa ga bin da nisantarsa yake wajaba akansa; domin kuwa mutum abin tambaya ne game da ayyukansa a ranar lahira.