عَنِ ابنِ مَسعُودٍ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«لَا يَحِلُّ دَمُ امْرِئٍ مُسْلِمٍ إِلَّا بِإِحْدَى ثَلَاثٍ: الثَّيِّبُ الزَّانِي، وَالنَّفْسُ بِالنَّفْسِ، وَالتَّارِكُ لِدِينِهِ المُفَارِقُ لِلْجَمَاعَةِ».
[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 1676]
المزيــد ...
Daga Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce:
«Jinin mutum musulmi ba ya halatta sai da ɗaya daga cikin abubuwa uku, bazawarin da ya yi zina, da ran (da ya kashe) rai, da wanda ya bar addininsa wanda ya bar jama'a».
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح مسلم - 1676]
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa jinin musulmi haramun ne, sai dai idan ya aikata ɗaya daga cikin ɗabi'un nan uku: Na farko: Wanda ya faɗa cikin alfashar zina, alhali ya riga ya yi aure da ƙulla ingantaccen ɗaurin aure, to sai kashe shi ta hanyar jifa ya halatta. Na biyu: Wanda ya kashe tsararren rai da aka hana kashewa ba tare da wani haƙƙi ba, to sai a kashe shi da sharuɗɗansa. Na uku: Wanda ya fita daga cikin jama'ar muslmai; ko dai ta hanyar barin addininsa gabaɗayansa ta hanyar yin ridda, ko wanda ya bari ba tare da ridda ba ta hanyar barin sashinsa kamar 'yan tawaye, da 'yan fashi, da mayaƙa cikin Khwarij da wasunsu.