عَنْ عَبْدِ اللهِ بْنِ عُمَرَ رَضيَ اللهُ عنهُما قَالَ: مَرَرْنَا مَعَ رَسُولِ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَلَى الْحِجْرِ، فَقَالَ لَنَا رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«لَا تَدْخُلُوا مَسَاكِنَ الَّذِينَ ظَلَمُوا أَنْفُسَهُمْ، إِلَّا أَنْ تَكُونُوا بَاكِينَ؛ حَذَرًا أَنْ يُصِيبَكُمْ مِثْلُ مَا أَصَابَهُمْ» ثُمَّ زَجَرَ فَأَسْرَعَ حَتَّى خَلَّفَهَا.
[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 2980]
المزيــد ...
Daga Abdullahi ɗan Umar - Allah Ya yarda da su - ya ce: Mun wuce tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - akan Hijr (gidajen Samudawa), sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce mana:
"Kada ku shiga mazaunan waɗanda suka zalinci kawunansu, sai dai idan kun kasance kuna masu kuka; dan kiyayewa kada abinda ya samesu ya sameku". Sannan ya tsawatar sai ya yi gaggawa har ya wuce wurin ya tura shi baya.
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2980]
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da ya wuce gidajen Samudawa ya yi hani akan shiga gidajen waɗanda ake yi wa azaba waɗanda suka zalinci kawunansu ko zowa gidajen, saidai idan mai shiga ɗin ya zama yana mai kuka yana mai izina da su; dan jin tsoron abinda ya samesu na azaba ya same shi, sannan ya zaburi dabbarsa sai ya gaggauta har saida ya ƙetare su.