عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رضي الله عنه قَالَ: سَمِعْتُ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَقُولُ:
«يَقْبِضُ اللَّهُ الأَرْضَ، وَيَطْوِي السَّمَوَاتِ بِيَمِينِهِ، ثُمَّ يَقُولُ: أَنَا المَلِكُ، أَيْنَ مُلُوكُ الأَرْضِ».

[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa:
"Allah Zai damke kasa, Zai ninke sammai da hannunSa na dama, sannan Ya ce: Ni ne sarki, ina sarakunan kasa".

Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa Allah - Madaukakin sarki - a ranar Alkiyama Zai damke kasa Ya tattarota, Ya ninke sama da hannunSa na dama Ya ninke sashinta a saman sashi Ya tafiyar da ita Ya karar da ita, sannan Ya ce: Ni ne sarki, ina sarakunan kasa?!

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Malayalam Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand bushtu Asami السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Tinatarwa da cewa mulkin Allah Shi ne wanzajje kuma mulkin waninSa mai gushewa ne.
  2. Girman Allah da girman ikonSa da sarautarSa da cikar mulkinSa.