+ -

عَنْ عَائِشَةَ أُمِّ المُؤْمنين رَضيَ اللهُ عنها قَالَتْ: سَمِعْتُ رَسُولَ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَقُولُ:
«يُحْشَرُ النَّاسُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ حُفَاةً عُرَاةً غُرْلًا» قُلْتُ: يَا رَسُولَ اللهِ النِّسَاءُ وَالرِّجَالُ جَمِيعًا يَنْظُرُ بَعْضُهُمْ إِلَى بَعْضٍ؟ قَالَ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: «يَا عَائِشَةُ، الْأَمْرُ أَشَدُّ مِنْ أَنْ يَنْظُرَ بَعْضُهُمْ إِلَى بَعْضٍ».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 2859]
المزيــد ...

Daga Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa:
«‌Za'a tashi mutane a ranar Lahira marasa takalma tsirara kuma marasa kaciya». Na ce: Ya Manzon Allah! mata da maza baki ɗaya sashinsu yana kallon sashi? Sai (Manzon Allah) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: «‌Ya A'isha, al'amarin ya fi tsanani a ce sashinsu yana kallon sashi».

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2859]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya siffanta sashin abinda ke cikin ranar alƙiyama, kuma mutane za'a tarasu bayan tashinsu daga ƙaburburansu dan yin hisabi, kuma cewa halinsu zasu zama marasa takalma, tsirara babu tufafi, marasa kaciya kamar ranar da iyayensu suka haifesu, yayin da Uwar muminai Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ji hakan sai ta ce tana mai mamaki: Ya Manzon Allah ! maza da mata baki ɗayansu sashinsu yana kallon sashi?! Sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa: Sha'anin tsayuwar da taruwa bayan tashi daga mutuwa a cikinsa akwai tsorace-tsoracen da zai ɗauke hankalin mutane da idanuwansu daga kallan al'aurori.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Bayanin tsorace-tsoracen ranar Lahira, kuma cewa mutum a wannan ranar wani abu ba zai shagaltar da shi daga hisabinsa ba haka nan ayyukansa.
  2. Karfafawa cewa mutum ba zai afka cikin saɓo ba sai dai a halin rafkana; dan da zai tina girman wanda ya saɓawa ko uƙubarSa da bai rafkana ba daga tinaShi da kuma gode maSa da kyakkyawan bautarSa ko da ƙiftawar ido, saboda haka zaka ga ma'abota taron alƙiyama sun shagalta da kawunansu sashinsu ba ya kallon sashi.
  3. Tsananin kunyar mata a zamanin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, wannan Nana A'isha ce - Allah Ya yarda da ita - tana tambaya cikin kunya lokacin da ta ji cewa za'a tashi halitta tsirara maza da mata.
  4. Sindi ya ce: Kowanne mutum ya shagalta da al'amarinsa kuma bai san halin ɗan'uwansa ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kowane mutum daga cikinsu a wannan ranar sha'aninsa ya wadace shi}
  5. [Abasa: 37].
  6. Babu wani da zai iya juyawa zuwa ga al'aurar wani.
  7. Kaciya: Ita ga namiji ita ce: Yanke fatar da ta rufe hashafa, ta mace kuma ita ce: Yanke fatar da ke saman bigiren da azzakari yake shiga ya yi kama da ƙahon zakara.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Swahili Yaran Tailand Asami الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin
Kari