+ -

عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رَضيَ اللهُ عنهُ أَنَّ رَسُولَ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ:
«رُبَّ أَشْعَثَ مَدْفُوعٍ بِالْأَبْوَابِ لَوْ أَقْسَمَ عَلَى اللهِ لَأَبَرَّهُ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 2622]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -: Lallai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"Da yawa mutum daƙal-daƙal abin tunkuɗewa a ƙofofi, da a ce zai yi rantsuwa ga Allah da (Allah) Ya kuɓutar da shi".

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2622]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa akwai daga cikin mutane wanda gashin kansa a cukurkuɗe yake, ya yi ƙura, ba ya shafa masa mai, kuma ba ya yawan wanke shi, ba shi da wata daraja a wurin mutane dan haka suke ture shi a bakin ƙofofinsu, suna korarsa dan wulaƙanta shi; saidai cewa shi da ace zai yi rantsuwa akan faruwar wani abu da Allah Ya farar da abun, dan girmama shi da amsa roƙonsa, da kuma kiyaye shi daga warware rantsuwarsa, hakan saboda falalarsa da matsayinsa a wurin Allah.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Allah ba Ya duba zuwa surorin bawa saidai Yana duba zuwa zukata ne da ayyuka.
  2. Ya wajaba akan mutum ya kula da aikinsa da tsarkin zuciyarsa sama da kulawarsa ga jiinsa da tufafinsa.
  3. Kanƙar dakai ga Allah da miƙa wuya gare shi to hakan sababi ne na amsa addu'a, saboda haka; Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Yana kuɓutar da rantsuwar masu tsoronSa ɓoyayyu.
  4. Bayanin tarbiyyar Annabi ga mutane; dan kada sashinsu su wulaƙanta sashi.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Swahili Yaran Tamili Asami الهولندية الغوجاراتية الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin