عن سهل بن سعد الساعدي رضي الله عنه مرفوعاً: "لأعطين الراية غدا رجلا يحب الله ورسوله ويحبه الله ورسوله، يفتح الله على يديه، فبات الناس يدوكون ليلتهم أيهم يعطاها فلما أصبحوا غدوا على رسول الله صلى الله عليه وسلم كلهم يرجو أن يعطاها: فقال: أين علي بن أبي طالب؟ فقيل: هو يشتكي عينيه، فأرسلوا إليه فأتي به، فبصق في عينيه، ودعا له فبرأ كأن لم يكن به وجع، فأعطاه الراية فقال: انفذ على رسلك حتى تنزل بساحتهم، ثم ادعهم إلى الإسلام وأخبرهم بما يجب عليهم من حق الله تعالى فيه، فوالله لأن يهدي الله بك رجلا واحدا خير لك من حمر النعم".
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Sahal Dan Saidi zuwa ga Annabi : "Lallai gobe kuwa zan bada Tuta ga wani Mutumi da yake son Allah da Manzonsa, Allah da Manzonsa suke sonsa, kuma Allah bada Nasara a Hannunsa" sai Mutane suka kwana suna ta ta tunani waye zai bawa yayin da suka wayi gari sai ya ce: Ina Aliyu Dan Abi Dalib? sai aka ce yana fama da Ido, sai aka tura masa yazo, sai yai tofi a Idanun nasa kuma yayi masa Addua take ya warke kamar bai taba yi ba, sai ya ba shi tuta, sai ya ce ka ci gaba har sai ka sauka a fagen su, sannan ka kirasuzuwa Musulunci kuma ka basu labarin abinda ya wajaba akansu na hakkin Allah Madaukaki akansu, Kuma na Rantse da Allah Mutum daya ya shiryu ta hanyarka yafi Alkairi a gareka da kayi Sadaka da Jajayen Rakuma, "lallai gobe kuwa zan bada Tuta ga wani Mutumi da yake son Allah da Manzonsa, Allah da Manzonsa suke sonsa, kuma Allah bada Nasara a Hannunsa sai Mutane suka kwana suna ta ta tunani waye zai bawa yayin da suka wayi gari sai ya ce: Ina Aliyu Dan Abi Dalib? sai aka ce yana fama da Ido, sai aka tura masa yazo, sai yai tofi a Idanun nasa kuma yayi masa Addua take ya warke kamar bai taba yi ba, sai ya ba shi tuta, sai ya ce ka ci gaba har sai ka sauka a fagen su, sannan ka kirasuzuwa Musulunci kuma ka basu labarin abinda ya wajaba akansu na hakkin Allah Madaukaki akansu, Kuma na Rantse da Allah Mutum daya ya shiryu ta hanyarka yafi Alkairi a gareka da kayi Sadaka da Jajayen Rakuma
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Lallai cewa Annabi Yayiwa Sahabbansa Bushara da cin Nasara akan yahudawa daga gobe a hannun wani Mutum yana da Mai girma Kuma mai jibinta Al'amarinsa ga Allah da Manzonsa, sai sahabbai yi muranar hakan kowa yana burin ace shi ne sabida tsananin kwadayinsu da Alkairi, yayin da suka tafi akan lokacin sai Annabi ya nemi Ali kuma sai neman ya dace da cewa bashi da lafiya yana ciwon Ido bayan ya zo sai Annabi ya yi tofi a idonsa da yawunsa Mai Albarka sai ciwon da yake ji ya gushe guhewa ta baki daya kuma ya bashi Jagorancin Raundunar yaki, kuma ya Umarce shi da tafiya a hankali har ya isa shigen abokan gaba sannan ya nemi da su shiga Musulunci, to idan suka amsa masa kiransa sai ya basu labarin abinda ya wajaba akan musulmi na farillai, sannan ya bayyana wa Ali cewa Falalar Da'awa zuwa ga Allah kuma cewa Mai Da'awa idan ya dace wani ya shiryu a hannunsa mutum daya to wannan yafi Alkairi daga mafi tsadar Daukiyar Duniya, to ta yaya kake gani ace a hannunsa shiriyar mafi yawan Mutane daga haka.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Swahili الدرية
Manufofin Fassarorin