عن عائشةُ -رضي اللهُ عنها- مرفوعًا: «تُقْطَعُ الْيَدُ فِي رُبْعِ دِينَارٍ فَصَاعِداً».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Aisha -Allah ya yarda da ita- zuwa ga Annabi: "Ana yanke hannu akan rub'u dinar zuwa sama da haka".
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Allah Madaukaki ya tsare jinin mutane da mutuncinsu da dukiyoyinsu, da duk wani abu da zai tunkude masu barna masu ketare iyaka.sai Allah ya sanya yanke hannun da yake da shi ake yin sata ya zama ukubar wanda ya dauki dukiyar da take a boye;don yanke hannun ya zame masa kankarar zunubinsa, kuma don shi wanda yayi satar da wani ma wanda ba shi ba suyi nesa da aikata hakan,su tafi neman na kansu ta hanyar da shari'a ta yarda da ita,sai aiki ya yawaita, sai a sami sakamakon hakn,kasa ta ginu rayuka su daukaka, yana daga hikimar Allah Madaukaki,sanya dan adadi karami a matsayin abin da za'a yanke hannu in aka dauke shi,dayan hudun zinare daya,don kare dukiyoyi,da tsare rayuwa.don tsaro ya tabbata,zukata su nutsu,mutane su yada dukiyoyinsu don tsuwuri da neman karuwar arziki.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam
Manufofin Fassarorin