عن عائشة رضي الله عنها قالت: «دخلت هند بنت عُتْبَةَ- امرأَة أَبِي سفيان- على رسول الله صلى الله عليه وسلم فقالت: يا رسول الله، إنَّ أَبَا سُفْيَان رَجُلٌ شَحِيحٌ، لا يُعْطِيني من النفقة ما يكفيني ويكفي بَنِيَّ، إلاَّ ما أَخَذْتُ مِنْ مَالِهِ بِغَيْرِ عِلْمِهِ، فَهَلْ عَلَيَّ فِي ذَلِكَ مِنْ جُنَاحٍ؟ فَقَالَ رسول الله: خُذِي مِنْ مَالِهِ بِالْمَعْرُوفِ مَا يَكْفِيكِ وَيَكْفِي بَنِيكِ».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Aisha Allah ya yarda da ita tace: "Hindu 'yar Utbata - Matar Abu Sufyan- ta shigo wajen Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- sai tace: Ya Manzon Allah, Abu Sufryan ya kasance mutum ne mai rowa, ba ya bamu abin da zai ishe mu ni da 'ya'ya na sai dai in na dauka daga cikin dukiyarsa ba tare da saninsa ba. Shin ba laifi akan yin hakan? Sai Manzo tsira da amincin Allah yace: Dauki abin da zai ishe ki ke da 'ya'yanki daga cikin dukiyarsa ba tare da barna ba.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Hidu 'yar Utbata ta tambayi Manzo tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- cewa mijinta baya bata abin da zai ishe ta ita da 'ya'yanta shin ko zata iya dauk cikin dukiyarsa ba tare da saninsa ba? sai yayi mata fatawa da halarcin yin hakan amma kar ta wuce abin da zai ishe su.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam
Manufofin Fassarorin