عَنْ عُبَادَةَ بْنِ الصَّامِتِ رضي الله عنه أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ:
«لَا صَلَاةَ لِمَنْ لَمْ يَقْرَأْ بِفَاتِحَةِ الكِتَابِ».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 756]
المزيــد ...

Daga Ubadah dan Samit - Allah Ya yarda da shi - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"Babu sallah ga wanda bai karanta Fatiha ba".

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi] - [Sahih Al-Bukhari - 756]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa sallah ba ta inganta sai da karanta suratul Fatiha, ita rukuni ce daga rukunan sallah a kowace raka'a.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Wanin karatun Fatiha ba ya isarwa daga gareta tare da iko a kanta.
  2. Bacin raka'ar da ba'a karanta Fatiha a cikinta ba, daga mai ganganci da jahili da mai mantuwa; Domin cewa ita rukuni ce, rukunai ba sa saraya ta kowanne hali.
  3. Karatun Fatiha yana saraya daga mamu idan ya riski liman yana ruku'u.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (54)