عن عُبَادَةَ بْنِ الصَّامِت رضي الله عنه عن النبي صلى الله عليه وسلم قال: «لا صلاة لمن لم يَقْرَأْ بفاتحة الكتاب».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

An karbo daga Ubada Dan Al-samit Allah ya yarda dashi daga Annabi-tsira da amincin Allah su tabbata agareshi-yace:"Ba Sallah ga wanda bai karanta Fatiha ba".
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Surar Fatiha,itace Uwar Al-kur'ani kuma Ruhinsa,domin cewa ita ta tattare nau'ika na Godiya da siffofi Madaukaka na Allah Madaukaki,da kuma tabbatar da Mulki da Rinjaye,da Makoma da Sakamako,da Bauta da Nufi,kuma wadannan sune nau'ikan Tauhidi da Taklifi.Saboda haka aka wajabta karantata acikin kowace Raka'a,kuma ingancin Salla yake tsayawa abisa karantata,kuma aka kore tabbatuwar Salla da aka shara'anta ba tare da karantata ba,kuma abinda yake karfafa koruwar tabbatuwarta a Shari'a abinda Dan Huzaima ya fitar dashi daga Abi Huraira ya daga Hadisin zuwa ga Annabi shine"Salla bata isuwa ba tare da an karanta Fatiha a cikinta ba".An kebance Mamu daga wannan Hukunci idan ya samu Liman yana Ruku'u to sai yayi kabbarar harama sannan yayi Ruku'u kuma Fatiha ta fadi akansa a wannan raka'ar saboda wani Hadisi,kuma domin cewa shi bai riski mahallin karatuba shine tsayuwa.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Swahili bushtu Asami السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin