عن أبي هريرة رضي الله عنه عن النبي صلى الله عليه وسلم قال: إِنَّ اللهَ طَيِّبٌ لَا يَقْبَلُ إِلَّا طَيِّبًا، وَإِنَّ اللهَ أَمَرَ الْمُؤْمِنِينَ بِمَا أَمَرَ بِهِ الْمُرْسَلِينَ، فَقَالَ: {يَا أَيُّهَا الرُّسُلُ كُلُوا مِنَ الطَّيِّبَاتِ وَاعْمَلُوا صَالِحًا، إِنِّي بِمَا تَعْمَلُونَ عَلِيمٌ} [المؤمنون: 51] وَقَالَ: {يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا كُلُوا مِنْ طَيِّبَاتِ مَا رَزَقْنَاكُمْ} [البقرة: 172] ثُمَّ ذَكَرَ الرَّجُلَ يُطِيلُ السَّفَرَ أَشْعَثَ أَغْبَرَ، يَمُدُّ يَدَيْهِ إِلَى السَّمَاءِ، يَا رَبِّ، يَا رَبِّ، وَمَطْعَمُهُ حَرَامٌ، وَمَشْرَبُهُ حَرَامٌ، وَمَلْبَسُهُ حَرَامٌ، وَغُذِيَ بِالْحَرَامِ، فَأَنَّى يُسْتَجَابُ لِذَلِكَ؟.
[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira daga Annabi ya ce: "Lallai Allah Mai tsarki ne kuma baya karba sai mai Tsarki, kuma ya Umarci Muminai da duk abinda ya Umarci Mazanninsa sai ya ce:{Ya ku Manzanni kuci daga dadadan abubuwa kuma kuyi aiki nagari,lallai ni ina sane da abinda kuke aikatawa} [51] kuma ya ce: {Ya ku Masu Imani kuci daga dadadan abinda muka Azurtaku} [Bakara172] sannan Annabi ya fadi tsawatarwa ga Al'ummarsa daga Haram; sabida ya ambaci wani Mutum da yake yawaita tafiya, kuma acikin ayyukan alheri kamar hajji da Jihadi da kuma neman abinci, gashi budubudu yake gashinsa yayi kura sabida tsawon tafiyarsa a cikin bin Allah, kuma yana daga hannunsa sama da Addua yana rokon Allah da kuma kaskantar da kansa izuwa ga Allah, kuma tare da hakan an nisanta amsa masa wannan Adduar tasa, sabida Munin abinda yayi, ta yadda Abincinsa ya kasance Haram ne abun shansa Haram ne.
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

Lallai cewa Allah ya tsarkaka ga barin dukkan wata tawaya ko aibi, kuma ya sifanta da siffofin girma da kyau da kuma kamala, kuma babu ba'a kusantarsa da wata ciyarwa ko sadaka daga kudin haram ko kuma abinda yake akwai Shubha a cikinsa ko kuma da lalatacce daga cikin Abinci, kuma ya halastawa Muminai ci daga dukkan tsarkakan abubuwa, kamar yadda ya halasta wa Manzanni tare da yin aiki na gari da kuma godiya ga Allah akan Ni'amominsa, sannan Annabi ya bada labari cewa Allah Madaukaki yanason ciyarwa daga abu mai kyau kuma Allah bayason wasu ayyuka sai masu kyau kuma ayyuka basa inganta sai da bin dalili sau da kafa, sannan Annabi ya fadi tsawatarwa ga Al'ummarsa daga Haram; sabida ya ambaci wani Mutum da yake yawaita tafiya, kuma acikin ayyukan alheri kamar hajji da Jihadi da kuma neman abinci, gashi budubudu yake gashinsa yayi kura sabida tsawon tafiyarsa a cikin bin Allah, kuma yana daga hannunsa sama da Addua yana rokon Allah da kuma kaskantar da kansa izuwa ga Allah, kuma tare da hakan an nisanta amsa masa wannan Adduar tasa, sabida Munin abinda yayi, ta yadda Abincinsa ya kasance Haram ne abun shansa Haram ne.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin
Kari