+ -

عَنْ أَبِي الْجَعْدِ الضَّمْرِيِّ رَضيَ اللهُ عنهُ، وَكَانَتْ لَهُ صُحْبَةٌ، أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ:
«مَنْ تَرَكَ ثَلَاثَ جُمَعٍ تَهَاوُنًا بِهَا طَبَعَ اللَّهُ عَلَى قَلْبِهِ».

[صحيح] - [رواه أبو داود والترمذي والنسائي وابن ماجه وأحمد] - [سنن أبي داود: 1052]
المزيــد ...

Daga Abul Ja'ad al-Damri - Allah Ya yarda da shi -, kuma ya kasance sahabi ne, cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"Wanda ya bar Juma'o'i uku dan wulaƙantar da su Allah zai yi yumƙi akan zuciyarsa".

[Ingantacce ne] - - [سنن أبي داود - 1052]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi gargaɗi daga barin sallar Juma'a, kuma wanda ya bar sallar Juma'a sau uku dan sakaci da kasawa ba tare da wani uzuri ba Allah zai rufe zuciyarsa ta hanyar hana isar alheri gare shi .

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Ibnul Munzir ya hakaito Ijma'i akan cewa sallar Juma'a farilla ce ta aini (wato ta hau kan kowa).
  2. Narko akan wanda ya bar Juma'a dan sakaci shi ne Allah zai yi yumƙi akan zuciyarsa.
  3. Wanda ya bar Juma'a dan wani uzuri to shi ba ya shiga cikin narkon.
  4. Al-Shaukani ya ce: Faɗinsa: (Juma'o'i uku), yana ɗaukar cewa ana nufin faruwar barin kai tsaye daidai ne Juma'o'in a jere ne ko sun rarrabu, hatta da a ce duk shekara zai bar Juma'a ɗaya da Allah - Maɗaukakin sarki - Ya yi yumƙi akan zuciyarsa bayan ta uku shi ne zahirin hadisin, kuma zai iya ɗaukar cewa ana nufin Juma'o'i ukun a jere.
Fassara: Turanci Indonisiyanci Sinhalese Vietnam Swahili Asami الهولندية الغوجاراتية الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin