عَنِ ‌ابْنِ عَبَّاسٍ رضي الله عنهما قَالَ:
تَوَضَّأَ النَّبِيُّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ مَرَّةً مَرَّةً.

[صحيح] - [رواه البخاري] - [صحيح البخاري: 157]
المزيــد ...

Daga Ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce:
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi alwala sau ɗaiɗai.

[Ingantacce ne] - [Bukhari ne ya rawaito shi] - [Sahih Al-Bukhari - 157]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance a sashin lokutansa idan zai yi alwala sai ya wanke kowacce gaɓa daga gaɓɓan alwalarsa sau ɗaiɗai, sai ya wanke fuska - daga [cikin wanke fuska] akwai kuskurar baki da shaƙa ruwa - da hannaye da ƙafafuwa sau ɗaiɗai, wannan shi ne gwargwadon wajibi.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Wajibi a wanke gaɓɓai (shi ne) sau ɗaiɗai, abin da ya ƙaru, to, mustahabbi ne.
  2. Halaccin yin alwala sau ɗaiɗai a wasu lokuta
  3. Abin shar'anta wa a shafar kai (shi ne) sau ɗaiɗai.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (58)