عَنْ ‌عَبْدِ اللهِ بْنِ زَيْدٍ رضي الله عنه:
أَنَّ النَّبِيَّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ تَوَضَّأَ مَرَّتَيْنِ مَرَّتَيْنِ.

[صحيح] - [رواه البخاري] - [صحيح البخاري: 158]
المزيــد ...

Daga Abdullahi ɗan Zaid - Allah Ya yarda da shi -:
Lallai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi alwala sau biyu-biyu.

[Ingantacce ne] - [Bukhari ne ya rawaito shi] - [Sahih Al-Bukhari - 158]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance a wasu lokutansa idan zai yi alwala yana wanke Kowacce gaɓa daga gaɓɓan alwalarsa sau biyu, sai ya wanke fuska - daga cikin wankewar akwai kuskurar baki da shaƙa ruwa - da hannaye da ƙafafuwa sau biyu.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Wajibi a wanke gaɓɓan alwala (shi ne) sau ɗaya abin da ya ƙaru, to, shi mustahabbi ne.
  2. Halaccin alwala sau bibiyu a wasu lokutan.
  3. Abin shar'antawa a shafar kai (shi ne) sau ɗaya.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (58)