عَنْ حُذَيْفَةَ بْنِ اليَمَانِ رَضيَ اللهُ عنه:
أَنَّ النَّبِيَّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ كَانَ إِذَا أَرَادَ أَنْ يَنَامَ وَضَعَ يَدَهُ تَحْتَ رَأْسِهِ، ثُمَّ قَالَ: «اللَّهُمَّ قِنِي عَذَابَكَ يَوْمَ تَجْمَعُ أَوْ تَبْعَثُ عِبَادَكَ».

[صحيح] - [رواه الترمذي] - [سنن الترمذي: 3398]
المزيــد ...

Huzaifa Ibnul Yaman -Allah Ya yarda da shi -:
Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan ya yi nufin yin bacci yana sanya hannunsa ƙarƙashin kansa, sannan ya ce: «‌Ya Allah Ka kareni azabarKa ranar da zaKa tara ko zaka tashi bayinKa».

[Ingantacce ne] - [Tirmizi ne ya ruwaito shi] - [Sunan Tirmizi - 3398]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan ya kwanta dan yayi barci, sai ya shimfiɗa hannunsa na dama kuma ya sanya kundukukinsa (kumatunsa)na dama akansa, sai ya ce: «‌Ya Allah» Ubangijina «‌Ka kareni» Ka kiyayeni daga «‌azabarKa» da uƙubarKa «‌ranar da zaKa tara ko zaKa tashi bayinKa» a ranar hisabi, ranar alƙiyama.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Falalar wannan addu'ar mai albarka, kuma an so kiyayewa a kanta dan yin koyi da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
  2. An so kwanciya akan ɓarin jiki na dama.
  3. Sindi ya ce: Faɗinsa (Ya Allah Ka kareni azabarKa), a cikinsa cewa yana kamata ga mai hankali ya maida baccinsa tsani dan tina mutuwa da kuma tashi a bayanta.
  4. Kariya daga azabar Allah a ranar alƙiyama tana kasancewa ne da falalar Allah da kuma rahamarSa, ta hanyar dacewar bawa ga aiki na gari da kuma gafarar Allah ga bayinSa.
  5. Tawali'un Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ga Ubangijinsa kuma Majiɓincin al'amuransa - Allah Maɗaukakin sarki -.
  6. Tabbatar da taruwa da kuma makoma, kuma cewa mutane masu komawa ne zuwa ga Ubangijinsu dan ya yi musu hisabi akan ayyukansu, wanda ya samu alheri to ya godewa Allah - Maɗaukakin sarki -, wanda ya samu koma bayan haka to kada ya zargi kowa sai kansa, kawai su ne ayyukan bayi Allah Yana kiyaye musu su.
  7. Kwaɗayin sahabbai - Allah Ya yarda da su - akan bayanin halayen Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agagre shi - a baccinsa.
  8. Faɗinsa: "Sai ya sanya hannunsa na dama ƙarƙashin kundukukinsa" ya kasance daga al'adunsa - tsra da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ne damantawa a cikin kowane abu, sai dai abinda dalili ya zo akan saɓaninsa.
  9. Bacci akan ɓarin jiki na dama ya fi saurin farkawa saboda rashin tabbatar zuciya a cikin wannan halin, kuma ya fi sauƙi ga zuciya; domin ita zuciya a ɓangaren hagu take, da a ce bawa ya yi bacci akan ɓarin hagu zai cutar da zuciya dan nauyin gaɓɓai a kanta.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (33)