عَنْ سَلْمَانَ الْفَارِسِيِّ رَضيَ اللهُ عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«ثَلَاثَةٌ لَا يُكَلِّمُهُمُ اللَّهُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَلَا يُزَكِّيهِمْ وَلَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ: أُشَيْمِطٌ زَانٍ، وَعَائِلٌ مُسْتَكْبِرٌ، وَرَجُلٌ جَعَلَ اللَّهَ لَهُ بِضَاعَةً، فَلَا يَبِيعُ إِلَّا بِيَمِينِهِ وَلَا يَشْتَرِي إِلَّا بِيَمِينِهِ».
[صحيح] - [رواه الطبراني] - [المعجم الصغير: 821]
المزيــد ...
Daga Salmanul Farisi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
«Mutum uku Allah ba zai yi musu magana ba a ranar alƙiyama kuma ba zai tsarkakesu ba kuma suna da zaba mai raɗaɗi: Dattijo mazinaci, da talaka mai girman kai, da mutumin da ya sanya Allah wata haja, ba ya sayarwa kuma ba ya siya sai da rantsuwarsa».
[Ingantacce ne] - [Al-Tabrani Ya Rawaito shi]
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labari game da wasu nau’uka uku na mutane, waɗanda suka cancanci uƙubar Allah a ranar alƙiyama da uƙuba uku idan basu tuba ba, ko a gafarta musu uƙubar ba: Ta farko: Allah ba zai yi musu magana ba a ranar alƙiyama saboda tsananin fushinSa, kai zai bijire musu, ko Ya yi musu maganar da ba zata faranta musu rai ba kuma yana nuni akan fushinSa akansu. Ta biyu: Ba zai tsarkakesu ba kuma ba zai yabesu ba kuma ba zai tsarkakesu daga zunubai ba. Ta uku: Azaba mai sa ciwo mai tsanani a lahira ta tabbata agare su. Waɗannan sinfofin na mutane sune: Sinfi na farko: Babban mutum kuma yake afkawa a cikin alfashar zina. Na biyu: Talaka mara dukiya, amma tare da haka yake yi wa mutane girman kai. Na uku: Wanda yake yawan rantsuwa da Allah a cikin saye da siyarwa, sai ya wulaƙanta sunan Allah, kuma ya sanya shi tsani dan samun dukiya.