+ -

عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رَضيَ اللهُ عنه:
أَنَّهُ لَقِيَهُ النَّبِيُّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ فِي طَرِيقٍ مِنْ طُرُقِ الْمَدِينَةِ وَهُوَ جُنُبٌ، فَانْسَلَّ فَذَهَبَ فَاغْتَسَلَ، فَتَفَقَّدَهُ النَّبِيُّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، فَلَمَّا جَاءَهُ قَالَ: «أَيْنَ كُنْتَ يَا أَبَا هُرَيْرَةَ؟» قَالَ: يَا رَسُولَ اللهِ، لَقِيتَنِي وَأَنَا جُنُبٌ فَكَرِهْتُ أَنْ أُجَالِسَكَ حَتَّى أَغْتَسِلَ، فَقَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: «سُبْحَانَ اللهِ، إِنَّ الْمُؤْمِنَ لَا يَنْجُسُ».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 371]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -:
Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya haɗu da shi a wata hanya cikin hanyoyin Madina alhali shi yana da janaba, sai ya sulale ya tafi ya yi wanka, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bibiye shi, lokacin da ya zo masa sai ya ce: «‌Ina kake ya Abu Huraira?» sai ya ce: Ya Manzon Allah ka haɗu da ni alhali ni ina da janaba sai na ƙyamaci in zauna da kai har sai na yi wanka, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «‌Tsarki ya tabbata ga Allah, lallai mumini ba ya zama najasa».

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح مسلم - 371]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya haɗu da Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - a sashin hanyoyin Madina, Abu Huraira ya kasance yana da janaba, kuma yana daga cikin girmamawarsa ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ƙyamaci zama da shi da kuma hira da shi alhali shi yana kan wannan halin dan yana zatan cewa shi najasa ne, sai ya tafi a ɓoye ya yi wanka, sannan ya dawo, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tambaye shi ina ya tafi? Sai ya sanar da shi halin da yake ciki, kuma cewa shi ya ƙyamaci zama da shi ne alhali shi yana najasa saboda janabar (da ta same shi), sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi mamaki kuma ya ce masa: Lallai cewa mumini mai tsarki ne ba ya zama najasa akan kowane hali; a raye ko a mace.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Janaba kawai tana hana sallah ne da taɓa Alƙur'ani da kuma zama a cikin masallaci, amma bata hana zama tare da musulmai da kuma fuskantarsu, kuma mai janaba ba ya zama najasa saboda ita.
  2. Tsarkakar mumini a raye ko a mace.
  3. Girmama ma'abota falala, da ilimi, da salaha, da kuma zama da su akan yanayi mai kyau.
  4. Halaccin neman izinin mai bi ga wanda ake bi idan zai tafi, haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi wa Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - inkarin tafiyarsa ba tare da saninsa ba, hakan domin cewa neman izini yana daga cikin kyakkyawan ladabi.
  5. Faɗin: Subhanal Lahi, a lokacin yin mamaki.
  6. Halaccin zantar da mutum game da kansa da abinda ake jin kunya daga gare shi dan maslaha.
  7. Kafiri najasa ne, sai dai najasarsa ta ma'ana ce dan munin aƙidarsa.
  8. Nawawi ya ce: A cikin wannan hadisin akwai ladubba cewa malami idan ya ga daga wanda yake binsa wani al'amarin da yake jin tsoro a kansa wanda a cikinsa akwai saɓanin daidai to ya tambaye shi, kuma ya faɗa masa daidai, ya kuma bayyana masa hukuncinsa. Allah ne Mafi sani.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Swahili Yaran Tailand Asami الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin