عن أبي هريرة رضي الله عنه :"أنَّ النبي صلى الله عليه وسلم لَقِيَه في بَعض طُرُقِ المدينَة وهو جُنُبٌ، قال: فَانْخَنَسْتُ مِنه، فذهبت فَاغْتَسَلْتُ ثم جِئْتُ، فقال: أين كنت يا أبا هريرة؟ قال: كُنتُ جُنُبًا فَكَرِهتُ أن أُجَالِسَك على غيرِ طَهَارَة، فقال: سبحان الله، إِنَّ المُؤمِنَ لا يَنجُس".
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

An karbo daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi - marfu'i: "lallai Annabi tsira da amincin Allah ya hadu da shi a wata hanya ta Madina alhali yana da janaba. sai yace: sai na sulale daga wajen shi, sai na tafi na yi wanka sannan na dawo, sai Annabi ya ce: ina kaje ya Aba Huraira? sai ya ce: Na kasance cikin janaba sai na kyamaci in zauna awajenka alhalin ba ni da tsarki, sai yace: subhanallah ai mumini baya kasancewa najasa
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Abu Huraira ya hadu da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a wata hanya ta Madina, a lokacin kuma Abu HUraira yana da janaba a jikinsa, sa yaki ya zauna a wajen Annabi yana a wannan halin, sai ya sulale a boye daga wajen Annabi ya je ya yi wanka sannan ya dawo. sai Annabi ya tambaye shi ina ya je, sai Abu Huraira ya baiwa Annab labarin halin da yake ciki, cewar bazai iya zama a wajen Manzo ba alhali da janaba a jikinsa, sai Annabi ya yi mamakin Abu Huraira da ya tsammaci kaasantuwan mai janaba naja sa ne, har ya tafi ya yi wanka ya kuma zo ya bashi labari, tare da cewa mumini ba zai taba zama najasa ba

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin