+ -

عَنِ ابْنِ عُمَرَ رَضيَ اللهُ عنهما قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«إِنَّ أَحَبَّ أَسْمَائِكُمْ إِلَى اللهِ عَبْدُ اللهِ وَعَبْدُ الرَّحْمَنِ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 2132]
المزيــد ...

Daga ɗan Umar - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce:
"Lallai ne mafi soyuwar sunayenku a wurin Allah (su ne) Abdullahi da Abdurrahman".

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2132]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa mafi soyuwar sunaye a wurin Allah su ne a ambaci namiji da: Abdullahi, ko: Abdurrahman.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. AlƘurɗubi ya ce: Za'a riskar da waɗannan sunayen a abinda ya kasance tamkarsu, kamar Abdurrahim da Abdulmalik da Abdussamad, kaɗai sun kasance mafi soyuwa zuwa ga Allah ne, domin cewa su sun ƙunshi abinda yake shi ne siffa ta wajibi ga Allah da abinda yake shi ne siffa ga mutum kuma wajibi gare shi, shi ne bauta, sannan aka raɓa bawa zuwa ga Ubangiji, raɓawa ta haƙiƙa sai ta gasgata ɗaiɗaikun waɗannan sunayen kuma suka ɗaukaka da wannan jerin, sai wannan falalar ta tabbata garesu. Waninsa kuma ya ce: Hikima a cikin taƙaituwa akan sunaye biyu cewa a cikin Alƙur'ani raɓa bawa zuwa wani suna daga cikn sunayen Allah - Maɗƙaukakin sarki - bai afkuba banda biyun nan, Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Lallai cewa shi yayin da bawan Allah ya tsaya yana kiransa}, kuma Ya fada a cikin wata ayar daban: {Kuma bayin Ubangiji Arrahman}, kuma fadinSa - Madaukakin sarki - Yana karfafa shi: {Ka ce ku kira Allah ko ku kira Arrahman}.
Fassara: Turanci Indonisiyanci Sinhalese Vietnam Swahili Asami الهولندية الغوجاراتية الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin