عَنْ عَبْدِ اللهِ بنِ مَسْعُودٍ رَضيَ اللهُ عنهُ قَالَ: نَامَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَلَى حَصِيرٍ، فَقَامَ وَقَدْ أَثَّرَ فِي جَنْبِهِ، فَقُلْنَا: يَا رَسُولَ اللهِ، لَوِ اتَّخَذْنَا لَكَ وِطَاءً، فَقَالَ:
«مَا لِي وَلِلدُّنْيَا، مَا أَنَا فِي الدُّنْيَا إِلاَّ كَرَاكِبٍ اسْتَظَلَّ تَحْتَ شَجَرَةٍ ثُمَّ رَاحَ وَتَرَكَهَا».
[صحيح] - [رواه الترمذي وابن ماجه] - [سنن الترمذي: 2377]
المزيــد ...
Daga Abdullahi ɗan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi bacci akan wata tabarma, sai ya tashi haƙiƙa ta yi masa tabo a gefensa, sai muka ce: Ya manzon Allah, inama dai a ce mun yi shimfiɗa saboda kai, sai ya ce:
"Matsayina da duniya, ni a cikinta ba komai bane sai kamar matafiyi ne akan abin hawa da ya sha inuwa a ƙarƙashin wata bishiya sannan ya tafi ya barta".
[Ingantacce ne] - - [سنن الترمذي - 2377]
Abdullahi ɗan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ambaci cewa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi bacci akan shimfiɗa ƙarama wacce aka saƙata da wasu daga tsirrai, sai ya miƙe alhali tabarmar ta yi tabo a fatar gefensa, sai muka ce: Ya manzon Allah, ina ma dai a ce mu yi maka wata shimfiɗa mai laushi da hakan ya fi kyau daga kwanciyarka akan wannan tabarmar mai kaushi, sai (annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Ni bana son sabo da duniya har in yi kwaɗayi a cikinta, kwatankwacina da wanzuwa a cikin duniya bai zama ba sai kamar wani matafiyi ne da ya sha inuwa ƙarƙashin wata bishiya sannan ya tafi ya barta.