عَنْ أَنَسِ بْنِ مَالِكٍ رَضيَ اللهُ عَنْهُ قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«مَنْ صَلَّى صَلاَتَنَا وَاسْتَقْبَلَ قِبْلَتَنَا وَأَكَلَ ذَبِيحَتَنَا فَذَلِكَ المُسْلِمُ الَّذِي لَهُ ذِمَّةُ اللَّهِ وَذِمَّةُ رَسُولِهِ، فَلاَ تُخْفِرُوا اللَّهَ فِي ذِمَّتِهِ».
[صحيح] - [رواه البخاري] - [صحيح البخاري: 391]
المزيــد ...
Daga Anas Ibnu Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
«Wanda ya sallaci irin sallarmu kuma ya fuskanci alƙiblarmu, kuma ya ci yankanmu to wannan shine muslmin da yake da alƙawarin Allah da alƙawarin ManzonSa, dan haka kada ku warware alƙawarin Allah».
[Ingantacce ne] - [Buhari ne ya rawaito shi] - [صحيح البخاري - 391]
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa wanda ya lazimci shari'un addini na zahiri cewa ya yi irin sallarmu, kuma ya fuskanci alƙiblarmu, kuma ya ci yankanmu yana mai halatta shi ; to wannan shine musulmin da yake da amanar Allah da ManzonSa da kuma alƙawarinSa, dan haka kada ku warware amanar Allah da alƙawarinSa a cikinsa.