عن أبي سعيد الخُدْريِّ رضي الله عنه قال: "كنا نعطيها في زمن رسول الله صلى الله عليه وسلم صاعًا من طعام، أو صاعًا من شعير، أو صاعًا من أَقِطٍ، أو صاعًا من زبيب، فلما جاء معاوية، وجاءت السَّمْرَاءُ، قال: أرى مُدّاً من هذه يعدل مُدَّيْنِ. قال أبو سعيد: أما أنا: فلا أزال أخرجه كما كنت أخرجه على عهد رسول الله صلى الله عليه وسلم ".
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Ab Sa'id Alkhudri -Allah Ya yarda da shi ya ce- "Mun kasance muna bada ita a lokacin Annabi Kwano daya na Abinci, ko kwano daya na Acca, ko kwano daya na cukui, ko kwano daya na zabibi yayin da Mu'awiya yazo sai aka same ta baki baki (sabida fari) sai ya ce: ina ganin Mudu daya na wannan a matsayin biyu na wannan. Sai Abu Sa'id ya ce: amma ni dai ban gushe ba ina futar da ita kamar yadda take a lokacin Annabi"
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Abu Sai'd yana bada labari cewa Mutane sun kasance suna bada zakkar fidda kai a lokacin Annabi Kwano daya na abinci amma yayin da Mu'awiya ya zo Madina a lokacin Mulkinsa, sai ya ce: ni ina ganin rabin kwanon Alkama yar sham yayi daidai da kwano daya na watar ta, sai Mutane suka dauki Maganarsa, amma Abu Sa'id sai yaki wannan ra'ayin kuma ya lazamtawa kansa ya futar da kwano dayansa daga kowane irin abinci kamar yadda ya kasance yana futarwa a lokacin Annabi, sabida fifita biyayya ga Annabi, kuma don ya bada sadakarsa mafi yawar da ake bukata.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin