عَنْ عَبْدِ اللَّهِ بْنِ يَزِيدَ الخَطْمِيِّ قَالَ: حَدَّثَنِي البَرَاءُ وَهُوَ غَيْرُ كَذُوبٍ، قَالَ:
كَانَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ إِذَا قَالَ: سَمِعَ اللَّهُ لِمَنْ حَمِدَهُ، لَمْ يَحْنِ أَحَدٌ مِنَّا ظَهْرَهُ حَتَّى يَقَعَ النَّبِيُّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ سَاجِدًا، ثُمَّ نَقَعُ سُجُودًا بَعْدَهُ.
[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 690]
المزيــد ...
Daga Abdullahi bn Yazid al-Khaɗmi ya ce: Bara'u ya zantar da ni alhali shi ba maƙaryaci ba ne, ya ce:
Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan ya ce: Sami'allahu liman hamidahu (Allah Yaji wanda ya gode maSa) wani ɗaya daga cikinmu baya sunkuyar da bayansa har sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya faɗi yana mai sujjada, sai muma mu faɗi muna masu sujjada a bayansa.
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح البخاري - 690]
Bara'au Dan Azib - Allah Ya yarda da shi - yana bada labari alhali shi mai gaskiyane, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan ya ɗago kansa daga ruku'u kuma ya ce: Sami'al lahu liman hamidahu (Allah Yaji wanda ya gode maSa), wanda ke bayansa ba ya gushewa a tsaye, kuma wani ba ya sunkuyar da bayansa dan yin sujjada har sai (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya sanya goshinsa akan ƙasa, sannan su faɗi suna masu sujjada a bayansa.