+ -

عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رَضيَ اللهُ عنه قَالَ:
جَاءَ رَجُلٌ إِلَى رَسُولِ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، فَقَالَ: يَا رَسُولَ اللهِ، أَرَأَيْتَ إِنْ جَاءَ رَجُلٌ يُرِيدُ أَخْذَ مَالِي؟ قَالَ: «فَلَا تُعْطِهِ مَالَكَ» قَالَ: أَرَأَيْتَ إِنْ قَاتَلَنِي؟ قَالَ: «قَاتِلْهُ» قَالَ: أَرَأَيْتَ إِنْ قَتَلَنِي؟ قَالَ: «فَأَنْتَ شَهِيدٌ»، قَالَ: أَرَأَيْتَ إِنْ قَتَلْتُهُ؟ قَالَ: «هُوَ فِي النَّارِ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 140]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce:
Wani mutum ya zo wurin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - sai ya ce: Ya Manzon Allah, shin kana ganin idan wani mutum ya zo yana son karɓar kuɗina? Ya ce: «‌Kada ka ba shi kuɗinka)) Ya ce: Shin kana ganin idan ya yaƙe ni? Ya ce: «‌Ka yaƙe shi» Ya ce: Shin kana ganin idan ya kashe ni? Ya ce: «‌Kai shahidi ne». Ya ce: Shin kana ganin idan na kashe shi ? Ya ce: «‌Shi yana cikin wuta»

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 140]

Bayani

Wani mutum ya zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Ya Manzon Allah, shin kana ganin idan wani mutum ya zo yana son ƙwatar dukiyata? Ya ce: Bai wajaba ka miƙa wuya ka ba shi dukiyarka ba, ya ce: Shin kana ganin idan ya yaƙeni? Ya ce: Yana halatta gareka ka yaƙe shi, ya ce: Shin kana ganin idan ya kasheni fa? Ya ce: To kai shahidi ne, ya ce: Shin kana ganin idan na kashe shi fa? Ya ce: Shi ya cancanci a yi masa uƙuba a cikin wuta a ranar alƙiyama.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Nawawu ya ce: Kare Mutuncin matar mutum (daga faɗe) wajibi ne ba tare da wani saɓani ba, kuma a sha'anin kare kai da kisa to akwai saɓani a cikin mazahabarmu (Shafi’iyyah) da mazahabar wasunmu, kare dukiya ya halatta amma ba wajibi ba ne.
  2. Hadisin dalili ne akan cewa lallai ilmi (ya zama) kafin aiki, inda wannan sahabin ya tambayi Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga abinda yake wajaba a kansa kafin ya aikata shi .
  3. Yana kamata abi a hankali a kare kai daga ɗan ta’adda, farko ta hanyar wa'azi ko neman agaji kafin fara kashe shi, idan ya fara yakar shi to lallai ƙoƙarinsa ya zama kare kai ne ba wai kisan ba.
  4. Jinin musulmi da dukiyarsa da kuma mutuncinsa to haramun ne.
  5. Nawawi ya ce: Ka sani cewa shahidi ya kasu gida uku;
  6. Na farkonsu wanda aka kashe a yaƙar kafirai, saboda wani sababi daga cikin sabubban yaƙi, to wannan yana da hukuncin shahidai a ladan lahira da kuma hukunce-hukuncen duniya, shi ne cewa ba za’a yi masa wanka ba kuma ba za’a yi masa sallah ba.
  7. Na biyu Shahidi a lada amma banda hukunce-hukuncen duniya, shi ne wanda ya mutu da ciwon ciki, da wanda aka kashe, da wanda gini ya faɗa masa, da wanda aka kashe dan kare dukiyarsa, da wasunsu daga waɗanda hadisai ingantattu suka zo da ambatansa shahidi, to wannan za’a yi masa, wanka za’a yi masa sallah, kuma shi a lahira yana da ladan shihidai, kuma baya lazimta ya zama yana da kwatankwacin ladan na farko.
  8. Na uku wanda ya saci ganima da makamancinta wanda hadisai suka zo da kore ambatansa shahidi idan an kashe shi a yaƙin kafirai, to wannan yana cikin shahidai a duniya, ba za’a yi masa wanka ba, kuma ba za’a yi masa sallah ba, kuma ba shi da ladansu cikakke a lahira.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Swahili Yaran Tailand Asami الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin