عن عبد الله بن عمر رضي الله عنهما قال: سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول: «مَن اقْتَنَى كَلْبًا -إلا كلبَ صَيْدٍ، أو مَاشِيَةٍ- فإنه يَنْقُصُ من أَجْرِهِ كل يوم قِيرَاطَانِ». قال سالم: وكان أبو هريرة يقول: «أو كلبَ حَرْثٍ»، وكان صَاحِبَ حَرْثٍ.
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abdullahi Dan Umar- Allah ya yarda da su- zuwa ga Annabi: "Duk wanda ya riki kare, to kullum ana rage masa kiradi biyu daga ladansa, sai dai in na farauta ne ko mai kula da dabbobi". Sai Salim yace: Abu Huraira ya kasance yana yana cewa: " ko karen noma" Abu Huraira ya kasace manomi
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Kare na daga cikin kaskantattun kazaman dabbobi, don haka shari'a mai tsarki ta hana a ike shi sabo da gudun cutarwa da barna, kasancewar Mala'iku na yin nesa da gidan da yake da kare, hakanan saboda tsoratarwa da razanarwa da najasa da cutarwa, da kuma wauta . duk wanda ke da kare zaa ke rage wani abu mai girma cikin ladansa, kwatankwacinsa girman kiradi biyu, Allah shi ne mafi sani, saboda yin haka sabon Allah ne. Idan akwai bukatar yin hakan to babu laifi cikin daya daga abubuwa uku: Na daya: Gadin dabbobin da ake jiye musu tsoron kyarkeci da barayi. Na biyu: Gadin dabobi. Na uku: Don yin farauta. Don wadannan amfanunuka za'a iya rikar kare kuma ba wani zargi a kan mutum.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam
Manufofin Fassarorin