+ -

عَنْ أَنَسِ بْنِ مَالِكٍ رَضيَ اللهُ عنه قَالَ:
بَيْنَمَا نَحْنُ فِي الْمَسْجِدِ مَعَ رَسُولِ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ إِذْ جَاءَ أَعْرَابِيٌّ، فَقَامَ يَبُولُ فِي الْمَسْجِدِ، فَقَالَ أَصْحَابُ رَسُولِ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: مَهْ مَهْ، قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: «لَا تُزْرِمُوهُ، دَعُوهُ» فَتَرَكُوهُ حَتَّى بَالَ، ثُمَّ إِنَّ رَسُولَ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ دَعَاهُ فَقَالَ لَهُ: «إِنَّ هَذِهِ الْمَسَاجِدَ لَا تَصْلُحُ لِشَيْءٍ مِنْ هَذَا الْبَوْلِ، وَلَا الْقَذَرِ إِنَّمَا هِيَ لِذِكْرِ اللهِ عَزَّ وَجَلَّ، وَالصَّلَاةِ وَقِرَاءَةِ الْقُرْآنِ» أَوْ كَمَا قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ: فَأَمَرَ رَجُلًا مِنَ الْقَوْمِ فَجَاءَ بِدَلْوٍ مِنْ مَاءٍ فَشَنَّهُ عَلَيْهِ.

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 285]
المزيــد ...

Daga Anas Ibnu Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce:
Wata rana muna cikin masallaci tare da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ga wani balaraben ƙauye ya zo, sai ya miƙe yana fitsari a cikin masallaci, sai sahabban Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suka ce: Tsaya tsaya, sai ya ce: Sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «‌Kada ku yanke masa fitsarinsa, ku ƙyake shi» sai suka rabu da shi har saida ya gama fitsari, sannan Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kira shi sai ya ce masa: «‌Lallai waɗannan masallatan badan fitsari aka yi su ba, ko dan ƙazanta , kawai su dan ambatan Allah ne - Mai girma da ɗaukaka, da sallah da kuma karatun alƙur'ani» ko kamar yadda Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Sai ya umarci wani mutum daga cikin mutanen sai ya zo da guga na ruwa sai ya zuba a kansa.

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح مسلم - 285]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance a cikin masallacinsa a tare da shi akwai sahabbansa, sai wani balaraben ƙauye ya zo daga ƙauye, sai ya zauna yana yin fitsari a grfen masallaci. Sai sahabbai suka yi masa tsawa suka ce: Tsaya tsaya. Sai (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Ku ƙyale shi, kada ku yanke masa fitsarinsa, sai suka barshi har sai da ya gama.
Sannan (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kirashi sai ya ce masa: Lallai masallatai badan fitsari aka yi su ba, ko nau'ikan ƙazanta ba, kawai su dan ambatan Allah ne - Mai girma da ɗaukaka -, da sallah, da kuma karatun alƙur'ani da makamancin haka. Sai (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya umarci wani mutum daga cikin sahabbai sai ya zo da guga cike da ruwa sai ya zuba akan fitsarinsa a hankali.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Wajabcin girmama masallatai, da kuma tsaresu daga abinda ba ya kamata da su.
  2. Nawawi ya ce: A cikinsa akwai kiyaye masallatai da tsaftacesu daga ƙazanta da kaki, da ɗaga murya da rigima, da siye da siyarwa da sauran ƙulle-ƙullen abubuwa, da abinda ke da ma'anar haka.
  3. Sassautawa jahili da kuma sanar da shi abinda yake wajibinsa ba tare da tsanantawa ko cutarwa ba, idan bai zo da abinda ya saɓa ba, haka kawai dan wulaƙanci ko tsaurin kai.
  4. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance malami ne mai tausayi, kuma mai ladabtarwa ne mai tausasawa, kuma mai tarbiyyantarwa ne mai juriya.
  5. Kwaɗaitarwa akan raya ɗakunan Allah - Maɗaukakin sarki - da yin sallah da kuma karatun alƙur'ani da kuma ambatan Allah - Maɗaukakin sarki -.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Swahili Yaran Tailand Asami الأمهرية الدرية الرومانية المجرية الجورجية الخميرية الماراثية
Manufofin Fassarorin