lis din Hadisai
Ku dinga maimaita wannan Alƙur’anin, ina rantse muku da wanda ran Muhammad yake a hannunSa ya fi saurin kufcewa sama da raƙumin da ya ke a dabaibayi
عربي
Turanci
urdu
Mafi alherinku shi ne wanda ya koyi Alkur’ani kuma ya koyar da shi
عربي
Turanci
urdu
Duk wanda ya karanta wani harafi daga littafin Allah, to, yana da lada, kuma kowane lada za a ninkashi goma
عربي
Turanci
urdu
Kwatankwacin muminin da yake karanta AlKur'ani kamar gawasa ne, kanshinta mai dadi ne, kuma dandanonta mai dadi ne, kuma kwatankwacin muminin da ba ya karanta AlKur'ani kamar dabino ne ba shi da kanshi amma dandanonsa ma zaki ne
عربي
Turanci
urdu
Gangaran a karatun Alƙur'ani yana tare da manyan mala'iku masu biyayya ga Allah, kuma wanda yake karanta Alƙur'ani kuma yake guragura a cikinsa yana mai shan wuya to yana da lada biyu
عربي
Turanci
urdu
Za'a ce da ma'abocin Alkur’ani: Karanta ka daukaka, ka rera kamar yadda ka kasance kana rerawa a duniya, domin cewa matsayinka zai tasayane a karshen ayar da ka karantata
عربي
Turanci
urdu
Babu hassada sai a cikin mutum biyu: mutumin da Allah ya bashi kudi, sai ya yi mulkin halakar sa da gaskiya, da kuma mutumin da Allah ya bashi hikima da shi, don haka ya yanke hukunci ya kuma koyar da shi
عربي
Turanci
urdu
Ranar Al-kiyama za'a zo da Qur'ani da Ma'abotansa wadan da suke aiki da shi a cikin Duniya
عربي
Turanci
urdu
Lallai cewa Allah yana daga Darajar wasu Mutane da wannan littafin kuma ya sauke Darajar wasu
عربي
Turanci
urdu
Tir da xayansu da yake cewa Na manta Aya kaza da kaza, aa an mantar da shi ku riqa tuna Qur'ani, saboda shi ne mafi saurin mantawa daga zukatan Maza sama da Raquma
عربي
Turanci
urdu
Ku karanta Alqurani domin zai zo Ranar Alkiyama mai ceton Ma'abotansa
عربي
Turanci
urdu