+ -

عَنْ أُمِّ عَطِيَّةَ رَضيَ اللهُ عنها قَالَتْ:
تُوُفِّيَتْ إِحْدَى بَنَاتِ النَّبِيِّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، فَخَرَجَ النَّبِيُّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ فَقَالَ: «اغْسِلْنَهَا ثَلاَثًا، أَوْ خَمْسًا أَوْ أَكْثَرَ مِنْ ذَلِكَ، إِنْ رَأَيْتُنَّ بِمَاءٍ وَسِدْرٍ، وَاجْعَلْنَ فِي الآخِرَةِ كَافُورًا -أَوْ شَيْئًا مِنْ كَافُورٍ-، فَإِذَا فَرَغْتُنَّ فَآذِنَّنِي»، قَالَتْ: فَلَمَّا فَرَغْنَا آذَنَّاهُ، فَأَلْقَى إِلَيْنَا حِقْوَهُ، فَقَالَ: «أَشْعِرْنَهَا إِيَّاهُ»، وَقَالَتْ: وَجَعَلْنَا رَأْسَهَا ثَلاَثَةَ قُرُونٍ.

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 1258]
المزيــد ...

Daga Ummu Aɗiyya - Allah Ya yarda da ita - ta ce:
Ɗaya daga cikin ’ya’yan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi mata - ta rasu, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fita sai ya ce: «Ku wanketa sau uku, ko sau biyar, ko sama da haka idan kuna ganin hakan, da ruwa da magarya, ku sanya kafur a na ƙarshe - ko wani abu daga kafur -, idan kun gama ku sanar da ni», ta ce: Yayin da muka gama sai muka sanar da shi, sai ya jeho mana mayafinsa, sai ya ce: «Ku sanya shi ɗanfare da jikinta», kuma ta ce: Kuma muka sanya kanta naɗi uku.

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح البخاري - 1258]

Bayani

Zainab 'yar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ta rasu, sai (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shiga wurin matan da zasu yi mata wanka, sai ya ce da su: Ku wanketa da ruwa da magarya mara sau uku, ko sau biyar ko sama da haka, idan akwai buƙatuwar hakan, ku sanya wani abu daga kafur a na ƙarshen, idan kun gama to ku sanar da ni. Yayin da suka gama wanketa sai suka sanar masa, sai ya baiwa masu wankewar mayafinsa, kuma ya ce: Ku yi mata likkafani a cikinsa kuma ku sanya shi shi ne tufan da zai bi jikinta, sannan aka tufka gashin kanta tufka uku.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Wajabcin wanke mamaci musulmi, kuma hakan Fardu kifaya ne.
  2. Mace ba mai wanketa sai mata, namiji ba mai wanke shi sai maza, sai abin da aka togance na mace tare da mijinta, da baiwa tare da mai ita, kowanne daga cikinsu yana da damar wanke ɗan'uwansa.
  3. Wankewar tana kasancewa ne da wanki uku, idan bai isa ba sai a yi biyar, idan bai isa ba, sai a yi ƙari akan haka gwargwadan maslaha da buƙata, bayan haka idan akwai wani abu na najasar da ya fito daga jiki, sai a toshe wurin da najasar ta fito daga gare shi .
  4. Mai wankewar yana yanke wankewar tasa akan mara, sau uku, ko sau biyar, ko sau akwai.
  5. Sindi ya ce: Hadisin yana nuni akan cewa babu iyakancewa a kan wanke mamaci, kai abin nema shine tsaftacewa saidai babu makawa a kula da mara.
  6. A samu magarya tare da ruwan; domin hakan yana tsaftacewa, kuma ana zare jikin mutum.
  7. Ana sa tirare a wankewa ta ƙarshe, dan kada ruwan ya tafi, kuma tiraren ya zama na kafur, domin kafur - tare da daɗin ƙanshinsa - yana ƙarfafar jiki, dan haka ba zai yi saurin lalacewa ba.
  8. Farawa da wanke gaɓɓai maɗaukaka, su ne: Dama, da gaɓɓan alwala.
  9. An so taje kan mamaciya da kuma tufke kitson tufka uku, da kuma sanya shi a bayan mamaciyar.
  10. Halaccin taimakekeniya a wanke mamaci saidai babu wanda zai zo sai wanda ake buƙatar zuwansa.
  11. Tabarruki da abubuwan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - kamar tufansa, wannan wani abu ne da ya keɓance shi, dan haka ba za'a ƙetare shi ba zuwa waninsa ba cikin malamai da kuma salihai ba; domin waɗannan abubuwan tauƙifiyya ne, sahabbai basu aikata shi tare da waninsa ba ko sau ɗaya; kuma yin hakan tsani ne na shirka kuma fitina ce ga wanda aka nemi tabarrukin da shi.
  12. Halaccin wakilta mutum amintacce a cikin aikin da abin da aka aminta a kansa idan ya kasance ya cancanci wakiltawar.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Malayalam Yaran Tailand Asami الهولندية الغوجاراتية الدرية المجرية الجورجية المقدونية
Manufofin Fassarorin