عَنْ أَنَسِ بْنِ مَالِكٍ رَضيَ اللهُ عنهُ قَالَ:
لَمَّا نَزَلَتْ: {إِنَّا فَتَحْنَا لَكَ فَتْحًا مُبِينًا لِيَغْفِرَ لَكَ اللهُ} إِلَى قَوْلِهِ {فَوْزًا عَظِيمًا} [الفتح: ١-٥] مَرْجِعَهُ مِنَ الْحُدَيْبِيَةِ، وَهُمْ يُخَالِطُهُمُ الْحُزْنُ وَالْكَآبَةُ، وَقَدْ نَحَرَ الْهَدْيَ بِالْحُدَيْبِيَةِ، فَقَالَ: «لَقَدْ أُنْزِلَتْ عَلَيَّ آيَةٌ هِيَ أَحَبُّ إِلَيَّ مِنَ الدُّنْيَا جَمِيعًا».
[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 1786]
المزيــد ...
Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce:
Lokacin da waɗannan ayoyin suka sauka: {Lallai Mu mun yi maka buɗi buɗi mabayyani dan Allah Ya gafarta maka} har zuwa faɗinSa: {Rabo mai girma} [al-Fath: 1-5] lokacin dawowarsa daga Hudaibiyya, alhali su baƙin ciki da ɓacin rai yana cakuɗe da su, alhali haƙiƙa annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya soke hadayarsa a Hudaibiyya, sai ya ce: "Haƙiƙa an saukar mini da wata aya ita ce mafi soyuwa gareni daga duniya da abinda ke cikinta baki ɗaya".
[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 1786]
Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya bada labarin cewa lokacin da faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki - ya sauka ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: {Haƙiƙa mu mun yi maka buɗi buɗi mabayyani (1). Dan Allah Ya gafarta maka abinda ya gabata daga zunubinka da wanda ya jinkirta, kuma Ya cika ni'imarSa gareka kuma Ya shiryar da kai hanya madaidaiciya (2). Kuma Ya taimake ka taimako mai girma (3). Shi ne wanda Ya sanya nutsuwa a cikin zukatan muminai dan su ƙara imani tare da imaninsu, rundunonin sammai da ƙasa nasa ce, kuma Allah Ya kasance Masani Mai hikima (4). Dan ya shigar da muminai maza da mata aljannatai ƙoramu suna gudana ta ƙarƙashinsu suna masu dawwama a cikinsu kuma Ya kankare musu munananan ayyukansu hakan ya kasance rabo mai girma a wurin Allah} [al-Fath: 1-5]. A lokacin dawowarsa daga Hudaibiyya, su kuma sahabbai bakin ciki da bacin rai ya turnuke su, kuma an hana su yin Umarah, saboda abinda sulhun ya faru a kansa da kuma zatansu cewa sulhun ba’a yi shi akan maslahar musulmai ba, hakika kuma sun yanka hadaya a Hudaibiyya, sai (annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: Haƙiƙa an saukar mini da wata aya wacce ita ce mafi soyuwa gareni daga duniya bakiɗayanta sannan ya karantata.