عَنِ ‌ابْنِ عَبَّاسٍ رَضِيَ اللهُ عَنْهُمَا قَالَ:
كَانَ النَّبِيُّ صَلَّى اللهُ عَليهِ وَسَلَّمَ لا يَعْرِفُ فَصْلَ السُّورةِ حَتَّى تَنْزِلَ عَليْهِ {بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ}.

[صحيح] - [رواه أبو داود]
المزيــد ...

Daga Dan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce:
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance ba ya sanin rabewar sura har sai {Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai} ta sauka a gare shi.

Ingantacce ne - Abu Daud Ya Rawaito shi

Bayani

Dan Abbas - Allah Ya yarda da su - yana bayyana cewa surorin Alkur’ani sun kasance suna sauka ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - amma ba ya sanin rabewarsu da karewarsu har sai {Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai} ta sauka gareshi, sai ya san cewa surar da ta gabata an cikata, kuma cewa ita farko ce ga sabuwar sura.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Baslamalah ana rabewa da ita tsakanin surori, saidai tsakanin Suratul Anfal da Suratul Taubah.