عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ عَنِ النَّبِيِّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَقُولُ:
«تَهَادَوا تَحَابُّوا».
[حسن] - [رواه البخاري في الأدب المفرد وأبو يعلى والبيهقي] - [الأدب المفرد: 594]
المزيــد ...
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
«Ku yi wa juna kyauta, za ku so juna».
[Hasan ne] -
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kwaɗaitar akan cewa Musulmi tare da ɗan'uwansa su dinga yawan kyaututtuka, kuma kyauta tana daga cikin sabubban soyayya da haɗuwar zuciya.