عَنْ عُمَرَ بْنِ الخَطَّابِ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ:
أَنَّ رَجُلًا مِنَ اليَهُودِ قَالَ لَهُ: يَا أَمِيرَ المُؤْمِنِينَ، آيَةٌ فِي كِتَابِكُمْ تَقْرَؤُونَهَا، لَوْ عَلَيْنَا مَعْشَرَ اليَهُودِ نَزَلَتْ لاَتَّخَذْنَا ذَلِكَ اليَوْمَ عِيدًا، قَالَ: أَيُّ آيَةٍ؟ قَالَ: {اليَوْمَ أَكْمَلْتُ لَكُمْ دِينَكُمْ وَأَتْمَمْتُ عَلَيْكُمْ نِعْمَتِي وَرَضِيتُ لَكُمُ الإِسْلاَمَ دِينًا} [المائدة: 3] قَالَ عُمَرُ: قَدْ عَرَفْنَا ذَلِكَ اليَوْمَ، وَالمَكَانَ الَّذِي نَزَلَتْ فِيهِ عَلَى النَّبِيِّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، وَهُوَ قَائِمٌ بِعَرَفَةَ يَوْمَ جُمُعَةٍ.
[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 45]
المزيــد ...
Daga Umar Ibnul Khaɗɗab - Allah Ya yarda da shi -:
Cewa wani mutum daga cikin Yahudawa ya ce masa: Yakai sarkin muminai, Wata aya a cikin littafinku kuna karantata, da a ce agurinmu mu Yahudawa ta sauka da mun riƙi ranar idi, ya ce: Wacce aya ce? ya ce: {A yau ne na cika muku Addininku kuma na cika muku ni'imata kuma na yardar muku da Musulunci a matsayin Addini} [al-Ma'ida: 3] Umar ya ce: Haƙiƙa mun san wannan ranar, da gurin da ta sauka ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikinsa alhali shi yana tsaye a Arfa a ranar Juma'a.
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح البخاري - 45]
Wani mutum daga cikin Yahudawa ya zo gurin sarkin muminai Umar - Allah Ya yarda da shi - kuma ya ce masa: Wata aya ce da kuke karantata a cikin littafinku Alƙur'ani, da ace mu jama'ar Yahudawa ne ta sauka a garemu a cikin littafinmu Attaura da mun maida wannar ranar idin da zamu dinga taruwa da shi; dan godiya ga ni'imar saukar wannan ayar mai girma, sai Umar - Allah Ya yardada shi - yace masa: Wace aya ce? Ya ce: {Kuma yaune Na cika muku Addininku, kuma Na cika muku ni'imaTa kuma Na yarje muku musulunci a matsayin Addini} Sai Umar - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Haƙiƙa mun san wannan ranar, da gurin da ayar mai girma ta sauka a cikinsa, haƙiƙa ta saukane ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -a ranar idi, ita ce ranar Juma'a alhali shi yana tsaye a Arfa, kuma su ranaku biyu ne masu girma a wurin musulmai.