عن صَفِيَّةُ بِنْتُ حُيَيٍّ رضي الله عنها قالت: «كان النبي صلى الله عليه وسلم مُعْتَكِفًا، فَأَتَيْتُهُ أَزُورُهُ ليلا، فَحَدَّثْتُهُ، ثمَّ قُمْتُ لِأَنْقَلِبَ، فقام معي لِيَقْلِبَنِي -وكان مسكنها في دار أُسَامَةَ بن زَيْدٍ-، فَمَرَّ رَجُلاَنِ من الأنصار، فلما رأيا رسول الله صلى الله عليه وسلم أسرعا، فقال النبي صلى الله عليه وسلم : على رِسْلِكُمَا، إنها صَفِيَّةَ بِنْتُ حُيَيٍّ، فقالا: سبحان الله يا رسول الله، فقال: إن الشَّيْطَانَ يَجْرِي من ابن آدم مَجْرَى الدَّمِ، وإني خَشِيتُ أن يَقْذِفَ في قُلُوبِكُمَا شرا -أو قال شيئا-». وفي رواية: «أنها جاءَت تَزُورُهُ في اعْتِكَافِهِ في الْمَسْجِدِ، فِي العَشْرِ الأوَاخِرِ من رمضان، فتَحدَّثَتْ عنده ساعة، ثم قامت تَنقَلِبُ، فقام النبي صلى الله عليه وسلم معها يَقْلِبُهَا ، حتى إذا بَلَغَتْ باب المسجد عند باب أم سلمة...» ثم ذكره بمعناه.
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Safiyya Yar Huyai zuwa ga Annabi: "Annabi ya kasance yana i'itikafi sai nazo na ziyarce shi da daddare, sai mukai magana sannan na koma, sai ya tashi don ya rakani, kuma dakinta ya kasance a gidan Usama Dan Zaid, to sai sai wasu Mutane biyu suka wuce daga Mutanen Madina, yayin da suka ga Annabi sai sukai sauri sai Annabi ya ce musu, kuyi a hankali; ai matata Safiyya Yar huyayi ce, sai Suka ce tsaki ya tabbata ga Allah ya Manzon Allah, sai ya ce "ai lallai shaidan yana yawo ajikin Mutum ne kamar yadda jini yake yawo, kuma ina tsoron kada ya jefa wani abu a zuciyarku na sharri, ko ya ce wani abu daban" a wata riwayar kuma "Cewa ita tazo ta ziyarce shi a wajen I'itikafin sa a Masallaci, a goman karshe na Azumi to tai masa Magana wani dan lokaci, sannan ta tashi don ta tafi sai Annabi ya tashi tare da ita don ya raka ta har sai da ta isa kofar Masallaci dai dai kofar Ummusalama" sannan ya fadi Ma'anar wannan Hadisin.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Annabi Ya kasance yana E'itikafi a cikin kwanaki goman karshe na watan Azumi, cewa Matarsa Safiiya ta ziyarce shi a daya daga cikin dararen sai sukai magana wani lokaci, sannan sai ta tashi domin ta koma gidan ta, sai ya tashi tare da ita don ya rakata, kuma ya dauke mata kewa, sai wasu Mutane biyu daga cikin Mutanen Madina suka wuce, yayin da suka ga Annabi sai sukai sauri a tafiyar su sabida kunyar Annabi yayin da suka ganshi yana tare tare da Iyalinsa, sai ya ce da su ku tafi a hankali cewa ai ita Matata ce Safiyya, sai ce: Tsarki ya tabbata ga Allah kuma shin akwai abunda zai janyo mu munana maka zato, sai ya basu labari cewa: Lallai Shaidan yana matukar Kwadayin batar da Yan Adam, kuma yana da dama mai girma kan haka, domin cewa shi yana gudu ne a jiki kamar yadda jini yake yi, sabida buyan hanyar shigar tasa, da kuma hanyoyin nasa, kuma yaji tsoron kada ya jefa wani abu-Mara kyau- a zuciyar su

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Portuguese
Manufofin Fassarorin