+ -

عَنْ أَبِي سَعِيدٍ رَضيَ اللهُ عنه:
أَنَّ جِبْرِيلَ أَتَى النَّبِيَّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، فَقَالَ: يَا مُحَمَّدُ اشْتَكَيْتَ؟ فَقَالَ: «نَعَمْ» قَالَ: «بِاسْمِ اللهِ أَرْقِيكَ، مِنْ كُلِّ شَيْءٍ يُؤْذِيكَ، مِنْ شَرِّ كُلِّ نَفْسٍ أَوْ عَيْنِ حَاسِدٍ، اللهُ يَشْفِيكَ بِاسْمِ اللهِ أَرْقِيكَ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 2186]
المزيــد ...

Daga Abu Sa'id - Allah Ya yarda da shi -:
Cewa (Mala’ika) Jibril ya zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya ce: Ya Muhammad baka da lafiya ne? sai ya ce: «‌Eh» ya ce: «‌Da sunan Allah nake maka ruƙya, daga dukkan abinda zai cutar da kai, daga sharrin kowane rai ko maitar mai hassada, Allah Ya warkar da kai, da sunan Allah nake maka ruƙya».

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2186]

Bayani

Mala'ika Jibril - aminci ya tabbata agare shi - ya zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya tambaye shi: Ya Muhammad kana fama da rashin lafiya ne? Sai ya ce: Eh. Sai Mala’ika Jibril ya yi wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi masa ruƙya da faɗinsa: «‌Da sunan Allah» ina mai neman taimakonSa «‌Nake maka ruƙya» nake nema maka tsari. «‌Daga dukkan abinda yake cutar da kai» ƙarami ne ko babba. «‌Daga kowace rai» mummuna. «‌Ko maitar mai hassada» da ya kai gareka, Allah «‌Ya warkar da kai» kuma ya kareka daga dukkanin cutuka. «‌Da sunan Allah nake maka ruƙya» ya maimaita shi ne dan kai matuƙa, kuma ya fara da shi kuma ya rufe da shi dan nuni zuwa ga cewa babu wani mai amfanarwa sai Shi - tsarki ya tabbatar maSa -.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Halaccin labarta rashin lafiya dan bayanin waƙi'in hali ba dan babin rashin haƙuri da kai kuka ba.
  2. Ruƙya tana halatta da sharuɗɗan nan masu zuwa:
  3. 1- Ta zama da Alƙur'ani ne ko da ambatan sunan Allah - Maɗaukakin sarki - da kuma addu'o'in da aka shara'anta.
  4. 2- Ta zama da harshen larabci, ko da abinda ake sanin ma'anarsa daga wasu harsunan daban.
  5. 3- Ya ƙudirce cewa ruƙya ita akan kanta bata tasiri; kawai ita sababi ce daga cikin sabubban da basa tasiri sai da izinin Allah - Mai girma da ɗaukaka -.
  6. 4- Ta kaɗaita daga shirka, ko abinda aka haramta, ko bidi'a, ko abinda zai kai zuwa ga hakan.
  7. Tabbatar da cutar lambing baka ( ko maita), kuma cewa ita gaskiya ce, to yana kamata a nemi yin ruƙya daga gareta.
  8. An so yin ruƙya da abinda ya zo a cikin hadisi.
  9. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - kamar waninsa ne daga mutane, duk abinda yake samun waninsa na rashin lafiya zai iya samunsa.
  10. Kulawar Allah ga AnnabinSa- tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da kuma kiyayeShi, da wakilta mala'ikunSa da hakan.
Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Swahili Yaran Tailand Asami الرومانية المجرية الجورجية
Manufofin Fassarorin