+ -

عَنْ قَتَادَةَ قَالَ:
سُئِلَ أَنَسٌ كَيْفَ كَانَتْ قِرَاءَةُ النَّبِيِّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ؟ فَقَالَ: «كَانَتْ مَدًّا»، ثُمَّ قَرَأَ: {بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ} [الفاتحة: 1] يَمُدُّ بِبِسْمِ اللَّهِ، وَيَمُدُّ بِالرَّحْمَنِ، وَيَمُدُّ بِالرَّحِيمِ.

[صحيح] - [رواه البخاري] - [صحيح البخاري: 5046]
المزيــد ...

Daga Ƙatada ya ce:
An tambayi Anas yaya karatun Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yake? sai ya ce: «Ya kasance yana yin madda», sannan ya karanta: {Bismillahir rahmanir rahim}[al-Fatiha:1] yana yin maddar Bismillah, kuma yana yin maddar Al-Rahman, kuma yana yin maddar Al-Rahim.

[Ingantacce ne] - [Buhari ne ya rawaito shi] - [صحيح البخاري - 5046]

Bayani

An tambayi Anas ibnu Malik - Allah Ya yarda da shi - yaya karatun Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - na Alƙur'ani yake? sai ya ce: Ya kasance yana jan sautinsa da karatu ja; yana jan Lami kafin Ha'i na lafazin jalalah, kuma yana jan Mim wanda ke kafin Nun daga Al-Rahman, kuma yana jan Ha'i daga Al-Rahim.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Madda ita ce jan haruffan madda waɗanda yake sune: Alif da Wawun da kuma Ya'un, idan sun kasance masu ɗauri kuma kafinsu akwai wasalin da ya dace da su.
  2. Bayanin shiriyar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin karatun Alƙur'ani.
  3. Ɗabbaƙawa na ilimi na bayanin kaifiyyar karatun Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
  4. Sindi ya ce: Faɗinsa: (Yana jan sautinsa ja), wato yana tsawaita haruffan da suka dace ga tsawaitawa yana neman taimako da su akan Tadabburin ma'anonin Alƙur'ani da tinani da kuma gargaɗar da wanda zai wa'azantu.
  5. Muhimmancin sanin Tajwidi da kuma Ulumul Ƙur'an.
  6. Fahimtar nassosi ana komawa ne ga malamai kawai, kamar yadda aka tambayi Anas - Allah Ya yarda da shi - sai ya bayyanawa mai tambayar.
Fassara: Indonisiyanci Fassarar Bangaliyanci Vietnam Kurdawa Portuguese Yaran Tailand Asami الهولندية الدرية المجرية الجورجية المقدونية
Manufofin Fassarorin