عن أنس بن مالك رضي الله عنه أن رسول الله صلى الله عليه وسلم قال: «لما صوَّرَ اللهُ آدمَ في الجنة تركه ما شاء الله أن يتركه، فجعل إبليسُ يُطيفُ به، ينظر ما هو، فلما رآه أجوفَ عَرف أنه خُلِقَ خَلْقًا لا يَتَمالَك».
[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...

Wannan fassarar tana bukatar Karin bita da gyaran yare.

An rawaito daga Anas bn Malik -Allah ya yarda da shi- cewa Manzon ALlah ya ce: "Yayin da Allah ya suranta Annabi Adam a cikin Al-janna ya barshi lokacin da Allah ya so ya barshi, sai ya sanya Iblis yana kewaya shi, yana kallonsa, yayin da ya ganshi yana ciki sai ya san cewa shi ba zai iya Mallakar kansa ba"
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

Yayin da Allah ya halicci nAnnabi Adam a cikin Aljanna kuma ya tsara Surarsa, sai ya barshi wani lokaci bai busa masa rai ba, sai Iblis ya rika kewaye gefensa, yana Kallons; don yasan wane abu ne wannan, yayin da ya ga cikin sa babu komai, sai yasan cewa shi Halitta ce Mai rauni da ba zata iya juriya ba wajen Waswasinsa, ko ya san cewa shi zai iya zuwa da zunubi ta hanyar cikinsa, saboda haka aka zo masa ta hanyar Bishiya, ko kuma ya kasance ya sani cewa yasan Halitta mai ciki rarrauna ce, kuma wasu Mutane sun kasa gane fadinsa: "Cikin Al-janna" tare da cewa abunda ya zo cewa Allah ya halicci Annabi Adam daga bangarorin Kasa, sai ka amsa musu da cewa shi an barshi a haka ne har tsawon lokaci har kirarsa ta zamanto yadda zata iya Karbar Rai, sannan aka dauke shi zuwa Al-janna kuma aka busa Masa rai a cikinta.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa
Manufofin Fassarorin
Kari