عن أبي سعيد الخُدْري رضي الله عنه : «أن رسول الله صلى الله عليه وسلم كان يَعْتَكِفُ في العَشْرِ الأَوْسَطِ من رمضان. فاعتكف عامًا، حتى إذا كانت لَيْلَةَ إِحْدَى وَعِشْرِينَ -وهي اللَّيْلَةُ التي يخرج من صَبِيحَتِهَا من اعتكافه- قال: من اعتكف معي فَلْيَعْتَكِفِ العَشْرَ الأَوَاخِرَ فقد أُرِيتُ هَذِهِ اللَّيْلَةَ ثم أُنْسِيتُهَا، وقد رَأَيْتُنِي أَسْجُدُ فِي مَاءٍ وَطِينٍ من صَبِيحَتِهَا، فَالْتَمِسُوهَا فِي العَشْرِ الأَوَاخِرِ، والتمسوها في كل وِتْرٍ. فَمَطَرَتِ السَّمَاءُ تلك الليلة، وكان المسجد على عَرِيشٍ، فَوَكَفَ المسجد، فَأبْصَرَتْ عَيْنَايَ رسول الله صلى الله عليه وسلم وعلى جَبْهَتِهِ أَثَرُ المَاءِ وَالطِّين من صُبْحِ إحْدَى وَعشْرِيْنَ».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abu Sa'id -Allah ya yarda da shi- cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi cewa ya kasance yanayin E'itikafi a goman tsakiya na Ramalana wata shekara sai yai E'itikafi har sai da ranar Ashirin da daya ta o wacce ita ce rananar da yake futowa a safiyarta daga E'itikafin sa ya ce: "Duk wanda ai yi E'itikafi tare da ni to yayi a goman karshe, to hakika an nunamun wannan daren sannan kuma aka manatar da ni ita, kuma na ganni ina Sujada a ikin Ruwa da tabo a Asubar ta, to ku neme ta a goman karshe kuma ku neme ta a Mara na kowawane dare kuma Masallacin ya kasance rufin arbar dabino ne , to sai Masallacin yayi ta zuba to naga -Manzon Allah- da idanuna goshinsa alamar ruwa da tabo a Asubar ranar Ashirin da daya.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Abu Sa'id Al'khudri yana bada labari cewa Annabi ya kasance yana yin I'itikafin goman tsakiya na Azumi don neman daren lailatul kadari, sai wata shekara yayi -kamar yadda ya saba- har sai da adaren Ashirin da daya, ita ce ranar da yake futowa a safiyarta daga I'itikafinsa, sai ya san cewa lallai daren lailatul kadari tana goman karshe, sai yace da Sahabbansa: Duk wanda yayi I'itikafi tare da ni goman tsakiya, to ya zarce da I'itikafinsa, yayi a goman karshe, kuma ya bada labarin cewa Allah yanuna masa ita a Mafarkinsa sannan ya mantar da shi ita, sai dai ya ce kamar yagani a barcin wasu alamominta a cikin wannan shekarar su ne: Sujadarsa a cikin sallar Asuba akan tabo mai ruwa, to Allah ya gasgata Mafarkin Annabinsa, sai akayi ruwa a daren Ashirin da daya kuma ya kasance Masallacinsa an gina shi ne da yayin danga, kuma kututtudabino shi ne ginshikansa kuma rufinsa na ganyen Dabino ne, to sai Masallacin yayi ta zubar ruwa, sai Annabi yayi Sujada a safiyar Ashirin da daya, a cikin ruwa da tabo, Taisir Allam (349) Tanbih Al'afham (3/472) Ta'asis Al'ahkam 3/292

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin