عن عَبدُ اللَّهِ بنِ عَبَّاسٍ رضي الله عنهما قال: «بِتُّ عِندَ خَالَتِي مَيمُونَة، فَقَام النَبيَّ صلى الله عليه وسلم يُصَلِّي مِن اللَّيل، فَقُمتُ عَن يَسَارِه، فَأَخَذ بِرَأسِي فَأَقَامَنِي عن يَمِينِه».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

an karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah ya yarda dasu yace: "na kwana a wajan Gwaggwona Maimuna,sai Manzan Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya tashi da daddare yana salla,sai na tsaya a hagunsa.sai ya ruko kaina ya tsayar dani a damansa".
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Sahabi maigirma dan Abbas Allah ya yarda dasu ya bada labari cewa ya kwana a wajan Gwaggwonsa matar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, don yai tsinkayi da kansa yadda tsayuwar daren Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi take yayin da Manzan Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya tashi da daddare, sai dan Abbas ya tashi don yai salla tare dashi, sai ya zama a hagun Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi a matsayin mamu;saboda cewa dama ita tafi kuma itace wajan tsayuwar mamu daga liman in ya kasance shi kadai ne sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ruko kansa, ya jawo shi ta bayansa,sai ya tsayar dashi a damansa

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Portuguese
Manufofin Fassarorin