عن عائشة رضي الله عنها قالت: ((كُنْت أَغْسِلُ الْجَنَابَةَ مِنْ ثَوْبِ رَسُولِ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم فَيَخْرُجُ إلَى الصَّلاةِ، وَإِنَّ بُقَعَ الْمَاءِ فِي ثَوْبِهِ)). وَفِي رواية: ((لَقَدْ كُنْتُ أَفْرُكُهُ مِنْ ثَوْبِ رَسُولِ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم فَرْكاً، فَيُصَلِّي فِيهِ)).
[صحيح] - [الرواية الأولى: متفق عليه. الرواية الثانية: رواها مسلم]
المزيــد ...

Daga A`isha -Allah ya kara yarda a gareta- ta ce: ((Na kasance ina wanke janaba daga tufafin manzon Allah mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi sai ya sai ya fita izuwa masallaci, alhalin lallai akwai danshi a jikin tufafin nashi)). a cikin wata ruwayar kuma: ((Hakika na kasance ina kankare shi daga tufafin manzon Allah mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi kamkarewa, sai yayi sallah a cikin shi))An Hanamu bin raka Jana'iza amma kuma ba hanin dole ba
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

A`isha Allah ya kara yarda da ita tana ambatar: cewa maniyyin janaba ya kasance yana shafar tufafin manzon Allah mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi, wani lokacin yana kasancewa danye sai ta wankeshi daga tufafin da ruwa, sai ya fita zuwa salla, alhalin ruwan bai gama bushewa daga tufafin ba, wani lokacin daban kuma, maniyyin yana kasancewa busashshe, a wannan lokacin sai ta kankare shi daga tufafin nashi kankarewa, sai yayi salla a cikinsa.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin