عن قيس بن أبي حازم، قال: دخل أبو بكر الصديق رضي الله عنه على امرأة من أَحْمَسَ يقال لها: زينب، فرآها لا تتكلم. فقال: ما لها لا تتكلم؟ فقالوا: حَجَّتْ مصمِتةً ، فقال لها: تكلمي، فإن هذا لا يحل، هذا من عمل الجاهلية، فتكلمت.
[صحيح] - [رواه البخاري]
المزيــد ...

Wannan fassarar tana bukatar Karin bita da gyaran yare.

An rawaito daga Kais Bn Abi Hazim, ya ce: Sayyadin Abubakar -Allah ya yarda da shi- ya shiga wajen wata Mata daga Kabilar Ahmas ana kiranta da Zainab, sai ya ganta bata Magana? Sa suka ce: tayi rantsuwar Hajji ne ba tare da Magana ba, sai ya ce da ita: kiyi maganarki, cewa hakan bai halatta ba, wannan yana daga cikin aikin Jahiliyya, sai tayi Maganarta.
Ingantacce ne - Buhari ne ya rawaito shi

Bayani

Abubakar -Allah ya yarda da shi ya shiga wajen wata Mata a cikin Kabilar Ahmas sunan ta Zainab, sai ya sameta bata magana, sai ya tambayeta mai yasa bata magana sai suka ce: tayo Hajji ne bata Magana, sai ya ce da ita: kiyi maganarki, saboda barin maganar baki daya bai halatta ba; saboda cewa shi ya Kasance daga cikin Ibadun Jahiliyya sannan sai Musulunci ya Haramta shi, kuma shigar Namiji zuwa mace ba tare da zargi ba ko kadaita kamar yadda Sayyadina Abubakar yayi -Allah ya yarda da shi- ya halatta.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara
Manufofin Fassarorin