عن أنس بن مالك رضي الله عنه ، قال: «لمَّا كان اليوم الذي دَخَل فيه رسول الله صلى الله عليه وسلم المدينةَ أضاءَ منها كلُّ شيء، فلمَّا كان اليوم الذي مات فيه أَظْلَم منها كلُّ شيء، وما نَفَضْنا عن رسول الله صلى الله عليه وسلم الأيْدِي وإنَّا لفي دَفْنِه حتى أَنْكَرْنا قلوبَنا».
[صحيح] - [رواه الترمذي وابن ماجه وأحمد]
المزيــد ...

Wannan fassarar tana bukatar Karin bita da gyaran yare.

Daga Anas Bin Malik -Allah ya yarda da shi- ta ce: "Yayin da Manzon Allah SAW ya shiga Madina a cikinta kowane abu ya haskaka, kuma Ranar da ya rasu a cikinta kowane abu a cikinta yayi duhu, kuma bamu watsa kasa kan Kabarin Manzon Allah SAW da Hannayenmu, kuma Mu wajen rufeshi har sai da muka tsani Zukatanmu"
Ingantacce ne - Ibnu Majah ne ya Rawaito shi

Bayani

Anas Bin Malik yana bada Labari daga Manzon Allah SAW cewa shi yayin da ya shiga Madina Farkon Hijirasa daga Makka, komai ya haskaka, yayinda da kuma ya yi wafati komai yayi duhu kuma Duhun da Hasken da aka faxa a wannan Hadisin ana nufin na Ma'ana bana Zahiri ba, sannan ya ya bada labarin cewa yayin suka gama binneshi basu samu zukatansu kamar yadda suke ba a baya a lokacin Manzon Allah SAW yana raye, na hasken Imani da Tausayi da Haxin kai a tsakaninsu saboda yankewar Wahayi, da rashin Albarkar Zama da shi SAW.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Kurdawa
Manufofin Fassarorin