عن أبي المنهال سيار بن سلامة قال: (دَخَلتُ أنا وأبي علَى أبي بَرزَة الأسلمي، فقال له أبي: كيف كان النبي صلى الله عليه وسلم يصلي المَكْتُوبَة؟ فقال: كان يُصَلِّي الهَجِير -التي تدعونها الأولى- حِينَ تَدحَضُ الشَّمسُ. ويُصَلِّي العَصرَ ثم يَرجِعُ أَحَدُنَا إلى رَحلِه في أَقصَى المدينة والشَّمسُ حَيَّة، ونَسِيتُ ما قال في المَغرب. وكان يَسْتَحِبُّ أن يُؤَخِّر من العِشَاء التي تَدعُونَها العَتَمَة، وكان يَكرَه النَّوم قَبلَهَا، والحديث بَعدَها. وكان يَنْفَتِلُ من صَلَاة الغَدَاة حِين يَعرِفُ الرَّجُل جَلِيسَه، وكان يَقرَأ بِالسِتِّين إلى المائة).
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Wannan fassarar tana bukatar Karin bita da gyaran yare.

An rawaito daga Al-minhal Sayar Bn Salama ya ce: (Na shiga ni da Babana ga Abu baraza Al-aslami, sai ya ce da shi yaya Annabi SAW yake Sallar farilla? sai ya ce: ya Kasance yana Sallar Azahar -wacce suke kiranta ta farko- lokacin da Rana ta karya, kuma yana Sallatar La'asar sannan dayan mu ya dawo zuwa Masaukinsa a karshen Madina Rana tana nan, na manta abunda ya ce a Magriba, kuma ya Kasance yana son ya jinkirta Isha wacce muke kiranta Al-atama, kuma ya kasance yana kin ayi bacci kafinta, da kuma yin Magana Bayanta kuma ya kasance yana yana tafiya daga Sallar Asuba lokacin da Mutum zai iya gane na kusa da shi, kuma ya kasance yana Karanta Aya Sttin zuwa Dari.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Abu Barzah -Allah ya yarda da shi- ya fadi lokutan Sallar Farilla, Sai ya fara da cewa shi Annabi SAW ya Kasance yana Sallar Azahar, lokacin da Rana ta Karkata daga daga tsakiyar Sama zuwa Yamma, kuma wannan shi ne farkon lokacinta, kuma yana Sallar La'asar, sannan daya daga Masallatan ya dawo gidan sa a mafi nisan wuri daga Madina kuma Rana bata gushe ba tana nan, wannan shi ne farkon lokacinta, amma Magriba Mai riwayar ya manta abunda ya zo cikinta, kuma Nassoshi sun nuna haka Ijma'in Malamai kan cewa farkon lokacin ta da faduwar Rana, kuma Manzon Allah ya Kasance yana son ya jinkirta Isha, Saboda lokacinta wanda ya fi shi ne a Sallaceta a karshen lokacinta Na Mukhtari, kuma ya Kasance yana kin ayi Bacci kafinta don tsoron ya jinkirta ta daga lokacinta Mukhtari ko ya rasa Jam'i, da kuma tsoron bacci ya cimmasa da kuma barin Sallar dare kuma yana kin yin Hira bayanta saboda tsoron makara ga barin Sallar Asuba, ko rasa Sallar jam'i, Kamar yadda yana tafiya bayan Sallar Asuba, a lokacin da Mutum yana iya gane waye yake zaune a gefensa, tare da cewa zai Karanta a cikin sallarsa Aya Sittin zuwa dari, daga cikin abunda ya ke nuna cewa shi yana Sallatarta da duku duku.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Portuguese
Manufofin Fassarorin