عن عَائِشَة رضي الله عنها قالت: (لقد كان رسولُ الله صلى الله عليه وسلم يُصَلِّي الفَجر، فَيَشهَدُ معه نِسَاء مِن المُؤمِنَات، مُتَلَفِّعَاتٍ بِمُرُوطِهِنَّ، ثم يَرجِعْن إلى بُيُوتِهِنَّ مَا يُعْرِفُهُنَّ أحدٌ من الغَلَس).
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Aisha -Allah ya yarda da ita- tace: (Manzon Allah tsira da amincin Allah ya kasance yana sallar Asuba, Muminai mata suna zuwa lullube da mayafansu, sannan su koma gidajensu ba wanda ke gane su, saboda sauran duhun dare
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Aisha -Allah ya yarda da ita tana ambata mana cewa: Matan Sahabbai sun kasance suna lullube jikinsu da tufafinsu kuma su je sallar Asuba tare da Annabi tsira da aminci su tabbata a gare shi, kuma har su koma gidajensu ba mai gane su, duk da kasancewar haske ya dan fara bayyana, tare da sauran duhun. Littafin Taisiril Ahkam, na Malam Bassam, shafi na 86

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin