عن عبد الله بن عباس رضي الله عنه قال: «شَهِد عِندِي رِجَال مَرْضِيُون - وأَرْضَاهُم عِندِي عُمر- أنَّ النَبِي صلى الله عليه وسلم نَهَى عن الصَّلاة بَعد الصُّبح حتَّى تَطلُعَ الشَّمسُ، وبعد العصر حتَّى تَغرُب». وعن أبي سعيد رضي الله عنه عن رسول الله صلى الله عليه وسلم أنه قال: «لا صَلاَة بعد الصُّبح حتَّى تَرتَفِعَ الشَّمسُ، ولا صَلاَة بعد العَصرِ حتَّى تَغِيبَ الشَّمس».
[صحيح] - [حديث ابن عباس رضي الله عنه: متفق عليه. حديث أبي سعيد رضي الله عنه: متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abdullahi Dan Abbas -Allah ya yarda da shi- yace: wasu yardaddun mutane sun bada sheda a waje na -a guri na wanda yafi kowa a cikinsu shi ne Umar- cewa Annabi -tsira da aminci su tabbata a gare shi- ya hana yin sallar nafila marar dalili bayan Asuba har sai rana ta fito,da kuma bayan La'asar har sai rana ta fadi" Daga Abu Sa'id-Allah ya yarda da shi- daga -Manzo tsira da aminci su tabbbata a gare shi- ya ce:"ba'a yin sallar nafila bayan Asuba har sai rana ta hudo, hakanan bayan La'asar har sai ta fadi
Ingantacce ne - Buhari da Muslim suka rawaito shi da ruwayoyin sa

Bayani

Annabi -tsira da amincin Allah- ya hana yin salla bayan Asuba har sai rana ta fito ta daga gwargwadon tsawon mashi yadda ido zai iya ganinta,gwargwadon minti biyar zuwa sha biyar,gwargwadon yadda malamai suka yi bayani.Haka nan yayi hani ga salla bayan La'asar har sai rana ta fadi,gabanin sallar Magariba da 'yan mintintina,,saboda yayi kamanceceniya da mushirikai wanda ke bautaw rana lokacin fitowar ta ko faduwarta,kuma an hana yin kamanceceniya dasu wajen ibada,har yace duk wanda yayi kama da wasu jama'a to yana cikinsu.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Swahili
Manufofin Fassarorin