عن عبد الله بن عمر رضي الله عنهما قال: «قد أصاب عمر أرضًا بخيبر. فأتى النبي صلى الله عليه وسلم يستأمره فيها. فقال: يا رسول الله، إني أصبت أرضًا بخيبر، لم أُصِبْ مالًا قَطُّ هو أنفس عندي منه، فما تأمرني به؟ فقال: إن شِئْتَ حَبَّسْتَ أصلها، وتصدقت بها. قال: فتصدق بها، غير أنه لا يُباع أصلها، ولا يوهب، ولا يورث. قال: فتصدق عمر في الفقراء، وفي القربى، وفي الرقاب، وفي سبيل الله، وابن السبيل، والضيف. لا جناح على من وليها أن يأكل منها بالمعروف، أو يطعم صديقًا، غير مُتَمَوِّلٍ فيه»، وفي لفظ: «غير مُتَأثِّلٍ».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abdullahi Dan Umar -Allah ya yarda da shi- ya ce: "hakika Umar ya sami kasa a khaibar sai ya zo wa Annabi yana neman umarninsa game da ita. sai ya ce: Ya Manzon Allah, Lallai ni na Sami Kasa a Kahibar, kuma ban sami
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Umar Dan Khattab ya sami wata gona a Khaibar, kimarta rabo dari ne kuma ita ce mafi tsadar dukiyarsa, sabida kyawunta da kuma darajarta, kuma Sahabbai sun kasance suna rigen rige wajen yin ayyukan da ladansu zai wanzu sai ya zo Wajen Manzon Allah yana mai kwadayin yin aikin Alkairi irin wanda yake cikin fadin Allah: {Bazaku taba samun ladan Sadaka ba cikakke sai kun ciyar da abinda kuke so} yana neman shawara ta yadda zai yi wannan Sadaka domin Allah, to sai yai masa nuni da Mafi kyawun hanyoyin Sadaka, kuma shi ne yabar Asalin abin kuma yayi wakafinsa, sai Umar yayi hakan, kuma sai ta zamanto Wakafin ta yadda ba zai iya siyar da ita ba ko bayarwa, ko gadarwa, ko wanin hakan daga cikin abubuwan da wanda ya Mallaki abu yake yi, wadanda suke sanya Mulkin abu ya koma hannun wan, ko kuma ya zama Dalilin na komawar, kuma yayi Sadaka da ita ga Talakawa da Miskinai, da kuma Yan uwa, kuma ya fanso wanda yake bawa daga bauta, ko biyan Diyya ga wanda ga wanda ta hau kansa, ko kuma ya taimaki Masu Jahadi a tafarkin Allah da ita, ko kuma ya ciyar da Matafiyi wanda guzurinsa ya yanke zuwa garin da za shi, ko kuma ya ciyar da Bako, domin Girmama Bako yana daga cikin Imani da Allah Madaukaki, kuma kasancewar tana da bukatar wanda zai kula da ita kuma ya rika gyara ta da ban ruwa da noma, kuma da rashin laifi ga wanda yake kula da ita dan yaci wata bukatarsa a ciki gwargwadon bukata, kuma ya ciyar da wani abokinsa ba tare da ya dauki wani abu ba don tara kudi da ita sama da bukatarsa, domin daman ba'a sanya ta ba sai don ciyarwa a hanyoyin Alkairi da kuma kyautatawa, ba don neman kudi ba ko tara Dukiya. Fadakarwa: Wakafi dai shi ne Musulmi yayi Sadaka da wata Dukiya da zata rika bayar da wani amfani ga wasu bangarorin Alkairi, sai ya yi amfani da abinda ta bayar din amma amma Asalin Dukiya tana nan, Misalinsa Mutum yayi Wakafin Gona ga Talakawa, to Yayan Itatuwan da shukar da duk akayi a cikin gonar za'a rabar da shi ne ga Talakawan kuma gonar zata ci gaba da Zama a matsayin Hubusi.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin